Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-07@06:51:46 GMT

An Bukaci ‘Yan Su Matsa Kaimi Har Sai Anbiya su Hakokinsu

Published: 7th, March 2025 GMT

An Bukaci ‘Yan Su Matsa Kaimi Har Sai Anbiya su Hakokinsu

An Bukaci ‘yan fansho suyi gangami ganin jinkirin da ake samu wajen biyan su kudaden su.

An shawarci kungiyar ’yan fansho ta tarayya da ta zaburar da mambobinta kan jinkirin rage basussukan da gwamnatin tarayya ta amince da su.

Jami’in hulda da jama’a na kungiyar ’yan fansho na Jami’ar Ahmadu Bello Zariya, Alhaji Muhammad Mamman, ya bayar da wannan shawarar a matsayin martani ga rahotannin da ke cewa an dakatar da zanga-zangar da ake shirin yi kan lamarin, biyo bayan rokon da PTAD ta yi na a ba da damar tattaunawa.

Alhaji Muhammad Mamman wanda ya bayyana goyon bayansa ga tattaunawa da wa’adin makonni hudu da hukumar NIPOST reshen kungiyar ‘yan fansho ta kasa ta bayar ya ba da shawarar fadada taron kungiyoyin domin ganin an warware matsalolin da aka samu wajen biyan basussukan da ake bin su.

Ya ji takaicin yadda duk da alkawuran da hukumar ta yi na biyan kudaden alawus-alawus din, har yanzu wadanda suka yi ritaya ba su samu kudaden da kungiyoyin da abin ya shafa suka amince da su ba.

Alhaji Muhammad Mamman ya jaddada bukatar kungiyoyin su kai kara ga Majalisar Dokoki ta kasa, EFCC da ICPC idan har aka kasa cimma matsayar tattaunawa kan lamarin duba da yadda ake zargin karkatar da kudaden fansho a baya ba tare da isassun hukumcin da zai kawo gyara ga lamarin ba.

COV/ SULEIMAN KAURA

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Fedpoly Bauchi Ta Sanya Na’urorin Ɗaukan Hoto ‘CCTV’ Don Daƙile Satar Jarabawa Da Inganta Tsaro

Da ya ke magana kan ziyarar tawatar NBTE, Rector ɗin ya ce aikin sahalewa na da matuƙar muhimmanci domin gano irin ƙoƙari da azamar makaranta a cikin shekaru biyar da suka gabata da nufin tabbatar kayan koya da koyarwa da malamai suna nan kan tsarin da aka amince da tafiyar da su tun da farko.

Ya tabbatar da cewa kwasa-kwasai har guda 78 ne jami’an NBTE suka nazarta a yayin wannan ziyararz, “Tawagar sun gama aikin su na ziyarar, yanzu haka muna zaman jiran sakamakon bincike da bin sawun nasu ne,” ya ƙara shaida.

A nata ɓangaren, Dakta Fatima Umar, daraktan shirye-shiryen kwalejoji kuma jagorar tawagar na NBTE, ta buƙaci kwalejin Kimiyya da fasaha na gwamantin tarayya da ke Bauchi da ya maida hankali wajen magance matsalolin gine-gine da kuma giɓin ma’aikata.

Da take samun wakilcin Adesina Oluade, ta jero sauran matsalolin da ta gano kamar ƙarancin littafai na ɗalibi, mujallu na ilimi, rashin samar da wutar lantarki yadda ya kamata, inda ta ce bangarorin na buƙatar daukan matakan gaggawa.

Umar ta jaddada cewa tsarin sahalewa na da nufin ƙarfafa tabbatar da samar da ilimi mai ingancin da kyautata aiki, inda ta sha alwashin cewa kwamitin zai cigaba da yin gaskiya da adalci a yayin aikinsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fedpoly Bauchi Ta Sanya Na’urorin Ɗaukan Hoto ‘CCTV’ Don Daƙile Satar Jarabawa Da Inganta Tsaro
  • Nazarin CGTN: An Bukaci Kasa Da Kasa Su Bijirewa Cin Zali Daga Amurka
  • Wani Kwararre Ya Bukaci A Rungumi Fahasar Zamani Don Bunkasa Aikin Noma A Nijeriya
  • Araqchi: Iran ba ta da matsala game da tattaunawa amma ba za ta lamunci yi mata barazana ba
  • Amurka ta soke duk wata takardar izinin shiga kasar da aka baiwa ‘yan Sudan ta Kudu
  • Jinkirin Fansho: PTAD Ta Fadi Dalili, Ta Ce Za a Biya Kudaden Wannan Wata
  • An haramta wa Akpabio da Natasha tattaunawa da manema labarai
  • Yadda Musulman Nijeriya Suka Gabatar Da Bikin Ƙaramar Sallah Cikin Matsin Tattalin Arziƙi
  • Manyan Cibiyoyin Kudi Na Duniya Sun Yi Gargadai Akan Sabbin Kudaden Fito Na Amurka
  • Shugaban Kasar Iran Ya Fadawa Muhammad Bin Salman Kan Cewa Tehran Tana Shirin Kare Kanta