Aminiya:
2025-04-08@12:34:30 GMT

Fashewar tankar mai: Mutum 7 sun mutu, gonaki sun lalace a Neja

Published: 7th, March 2025 GMT

Aƙalla mutum bakwai ne suka rasa rayukansu a ranar Talata sakamakon fashewar wata tankar mai da ta tashi a Jihar Neja, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama tare da lalata filayen noma a cikin unguwanni.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Ƙaramin Rami da ke ƙaramar hukumar Mashegu da misalin ƙarfe 6:30 na yamma.

An yi garkuwa da ɗan uwan ​​Bishop Kukah da wasu 6 a Kaduna Najeriya ta kama hanyar gyaruwa – Remi Tinubu

Rahotanni sun bayyana cewa haɗarin ya afku ne lokacin da wata motar ɗaukar kaya ta yi yunƙurin kaucewa wasu munanan hanyoyi.

Waɗanda fashewar ɗin ta rutsa da su sun haɗa da: Rafiatu Sahabi da Ramlat Shehu da Rashida Abdullahi da Raliya Abdulrahman da Zainab Ahmed, Zuwaira Idrisu da kuma Maryam A. Nura.

Wata mata mai suna Maimuna Isah ta samu raunuka kuma tana karɓar magani a cibiyar kula da lafiya matakin farko na Saho Rami.

Motar tankar dai ta kife ne ta zubar da man cikinta a kan titi, inda man ya kwarara zuwa wani rafi da ke kusa inda manoman rani ke aikin noman shinkafa.

An bayyana cewa man da ya zube ya ci karo da wani famfunan ruwa da manoman ke amfani da su, lamarin da ya sa gobarar da ta koma kan tankar da ta kai ga fashewa.

Gobarar ta mamaye filayen noma ta kuma gurɓata rafin, inda ta ƙona manoma da dama da kuma ƙone gonakin shinkafa da kayan lambu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fashewar tankar mai

এছাড়াও পড়ুন:

Red Crescent ta Falasdinu ta nemi a yi bincike kan kisan da Isra’ila ta yi wa ma’aikatan agaji

Kungiyar agaji ta Red Crescent ta Falasdinu ta bukaci a gudanar da bincike mai zaman kansa kan kisan da Isra’ila ta yi wa ma’aikatan agaji a zirin Gaza, bayan da wasu sabbin hujjojin bidiyo suka nuna yadda sojojin Isra’ila suke harbin motocin daukar marasa lafiya.

Bidiyon da ya ci karo da wani nau’in lamarin da sojojin Isra’ila suka yi cewa “an gano wasu motoci marasa da yawa suna tunkarar sojojin Isra’ila ba tare da fitillu ko alamun motocin ambullance na gaggawa ba”.

Shugaban kungiyar agajin ta Falasdinu Younes al-Khatib, ya bukaci a gudanar da bincike mai zaman kansa kan kashe-kashen, yana mai jaddada cewa ba za a iya amincewa da binciken da sojojin Isra’ila ke jagoranta ba.

“Ba mu amince da duk wani binciken da sojojin suka yi ba, kuma wannan ne ya sa muka fito fili a kan cewa muna bukatar bincike mai zaman kansa kan lamarin,” in ji al-Khatib a wani taron manema labarai a hedkwatar Majalisar Dinkin Duniya da ke New York, yayin da yake magana kan harin da ya kashe likitoci da ma’aikatan jin kai 15 a Gaza.

Ya yi Allah wadai da karuwar hare-haren da ake kai wa ma’aikatan jin kai da wuraren aikinsu, yana mai jaddada cewa ana kai hari kan tambarin kungiyar agaji ta Red Crescent, wanda ya kamata a kiyaye a karkashin dokokin kasa da kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mahara sun yi garkuwa da fiye da mutum 50 a Katsina
  • Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 30 a Kongo
  • Saudiyya ta musanta hana ’yan Nijeriya biza
  • An sake kona Kur’ani mai tsarki a kasar Netherlands
  • Fedpoly Bauchi Ta Sanya Na’urorin Ɗaukan Hoto ‘CCTV’ Don Daƙile Satar Jarabawa Da Inganta Tsaro
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da hare-haren Filato, sun nemi a yi adalci
  • Ɓarawo ya haɗiye ɗan kunnen Naira biliyan ɗaya
  • Burtaniya Ta Soki Gwamnatin Netanyahu Kan Hana ‘Yan Majalisarta Biyu Shiga Cikin Isra’ila
  • Red Crescent ta Falasdinu ta nemi a yi bincike kan kisan da Isra’ila ta yi wa ma’aikatan agaji
  • Rashin ɗa’a: Gwamnatin Borno ta gargaɗi masu amfani da shafukan sada zumunta