A wani bincike mai kayatarwa da wani rukuni na masana kimiyya na kasar Sin ya gudanar, ya gano wasu tsare-tsaren gudanar da rayuwa, a muhallin halittu mafi zurfi cikin kwarin teku da ake cewa “Mariana Trench”. Wurin da ake ganin shi ne mafi zurfi a sassan tekunan duniyar nan.

Sakamakon binciken da aka wallafa a mujallar “journal Cell”, cikin wasu takardun bincike 3, ya bayyana cewa, ta amfani da na’urar nutso a karkashin teku mallakin kasar Sin mai suna Fendouzhe, masu nazarin kimiyyar sun gano tsare-tsaren gudanar rayuwa na musamman, da ma albarkatun dake tattare da kananan halittu dake rayuwa a wurin mai tsananin zurfi, da halittu dangin kaguwa, da dangin kifaye dake wurin.

Kazalika, sakamakon binciken ya baiwa bil adama damar kara fahimtar yanayin rayuwar halittu a muhallin karkashin teku da zurfinsa ya kai mita 10,000, yayin da nau’o’in kwayoyin halittu, da yanayinsu, da tasirin rayuwarsu, ka iya baiwa masu bincike damar gudanar da nazari bisa sabbin kirkire-kirkire, ta yadda za a kai ga magance tarin kalubale masu nasaba da albarkatun halittu masu rai. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rahoto: Yara Falasdinawa 350 ne Isra’ila ke tsare da su a gidajen kurkuku

A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, a yayin bikin ranar yara kanana ta duniya a Falasdinu, cibiyoyi masu fafutuka kan harkokin fursunoni sun sanar da cewa: Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila tana ci gaba da tsare kananan yara Palastinawa sama da 350 a gidajen yari da wuraren da ake tsare da fursunoni.

Sanarwar hadin gwiwa da hukumar kula da harkokin tsare-tsare, da “Kungiyar Fursunonin palasdinu”, da kuma “Cibiyar Kare Hakkokin Bil Adama ta Al-Dameer” suka fitar, ta bayyana cewa, yaran na fuskantar matsaloli Ciki har da azabtarwa, yunwa da gangan, da rashin kulawar likita.

Wadannan cibiyoyi sun jaddada cewa yaran Palasdinawa su ma suna fuskantar tauye hakkinsu, wanda irin wannan hali ne ya yi sanadin shahadar wani yaro a cikin makon nan a gidan yarin Isra’ila.

A cewar wadannan kungiyoyi, tsare yara bias irin wannan tsari na Isra’ila yana karuwa, kuma manufarsu ita ce kawar da yaran daga cikin iyalansu da lalata kuruciyarsu. Kuma wannan shi ne a lokacin da aka fi kai hare-hare mafi muni a tarihi kan yaran Palastinawa, yayin da ake ci gaba da kisan kiyashin, dubban yara ne suka yi shahada, wasu dubbai kuma suka jikkata ko kuma sun rasa iyalansu.

Kungiyoyin kare hakkin bil adama sun kuma sanar da cewa, tun bayan da aka fara kisan kiyashin, an samu sauye-sauye a halin da ake ciki na fursunoni yara.

Game da yara a Gaza, saboda ci gaba da tilsta manufar korar jama’a daga yankunansu da Isra’ila ke aiwatarwa, yara da dama sun rabu da iyalansu.

Duk da tsauraran matakan hana kai ziyara, kungiyoyin lauyoyi sun yi nasarar ganawa da wasu daga cikin yaran da ake tsare da su a gidajen yarin Ofer, Megiddo, da Damon, kuma an tattara shedu da dama da suka nuna irin yadda ake azabtar da su da kuma tauye hakki akan wadannan yaran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yan Sanda A Saudiya Sun Tsare Wata Bafalasdinya Saboda Bayyana Tutar Kasarta A Kan Jakarta A Masallacin Ka’aba
  • Tsofaffin Ma’aikatan FRCN Za Su Gudanar da Zanga-zanga Kan Jinkirin Biyan Hakkokin Su
  • Matakin Sin Na Karfafa Takaita Fitar Da Abubuwa Masu Alaka Da Ma’adanan “Rare Rarth” Na Nuni Ga Aniyarta Ta Kare Tsaron Kasa
  • Araqchi: Babu Wata Tattaunawa Da Aka Gudanar Tsakanin Amurka Da Iran
  • Rahoto: Yara Falasdinawa 350 ne Isra’ila ke tsare da su a gidajen kurkuku
  • An sayar da kare mafi tsada a duniya
  • Sin Ta Gabatar Da Dabarunta Na Raya Sana’o’i Da Fasahohi Masu Kiyaye Muhalli Ga Taron WTO
  • Ɓarawo ya haɗiye ɗan kunnen Naira biliyan ɗaya
  • Ba Rabo Da Gwani Ba: Abdullahi Karkuzu 1931-2025
  • Red Crescent ta Falasdinu ta nemi a yi bincike kan kisan da Isra’ila ta yi wa ma’aikatan agaji