NNPC Da Matatar Dangote Na Gasar Rage Farashin Fetur
Published: 7th, March 2025 GMT
“NNPC na amfani da kayayyakin da ake shigowa da su daga kasashen waje domin yin gogayya da matatar Dangote, a maimakon ta dukufa amfani da matatunta na mai da suke cikin kasar nan. Wannan lamarin na shafan dorewar musayar kasuwanci kuma zai kara janyo damuwowi ne kawai ga tattalin arzikin kasar nan,” Iledare ya shaida.
Wani masanin makamashi kuma shugaban NES, Farfesa Adeola Adenikinju, ya ce akwai bukatar hukumomi su dauki matakan da suka dace domin tabbatar da wadatar mai da kuma saukinsa a kasuwanni.
Ya kuma lura da cewa akwai bukatar magance dakile gasar rashin adalci domin a samu yin ciniki sosai a tsakanin masu mai.
Mataimakin shugaban IPMAN, Hammed Fashola, ya nuna farin ciki da rage farashin litar mai, wanda ya yi nuni da cewa mafi yawan ‘yan Nijeriya da ita suka dogara.
Ya tabbatar da cewa dillalan mai da dama sun fara sayar da mai a gidajen mansu kan farashin mai rahusan duk kuwa da cewa sun sayi mai din a farashi mai tsada.
Fashola ya ce, “Yayin da NNPCL ke sayar da mai kan lita guda a naira 860 a gidajen manta, amma sabon farashin bai nuna haka ba, amma ana ta kokarin sabuntawa.”
Duk kokarin jin ta bakin mai magana da yawun NNPC, Femi Soneye, ya citura.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Farashi
এছাড়াও পড়ুন:
Ƙin yin sulhu da ’yan bindiga na haifar da alheri – Gwamnan Zamfara
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ce matsayarsa na ƙin amincewa a yi sulhu da ’yan bindiga na taimakawa wajen dawo da zaman lafiya a jihar.
Ya bayyana haka ne a ranar Alhamis yayin da yake karɓi baƙuncin Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Hassan Bala Abubakar.
An kama ’yan Pakistan biyu da laifin yin garkuwa a Legas HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Sheikh Hassan Jingir a JosAir Marshal Abubakar, ya ziyarci jihar domin yin ta’aziyya harin bam da rundunar sojin sama ta kai wa wasu mutane bisa kuskure.
Gwamna Lawal ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta canza matsayarta ba game da ƙin sasanci da miyagun mutane.
“Muna shaida wa kowa cewa ba za mu zauna da ’yan bindiga ba,” in ji shi.
“Hanyar da muka ɗauka tana haifar da sakamako mai kyau, kuma muna ganin zaman lafiya yana samuwa a Zamfara.”
Gwamnan ya kuma yaba da yadda jami’an tsaro ke hanzarin amsa kiran gaggawa a jihar.
“Ina gode wa Hafsan Sojin Sama saboda matakin gaggawa da ya ɗauka. Kafin wannan ziyarar, ya aike da manyan jami’ai domin jajanta mana.
“Wannan yana nuna ƙwazo da jajircewarsu wajen kare lafiyar mutanenmu,” in ji shi.
Hakazalika, Gwamna Lawal ya bayyana cewa ana gina sabon filin jirgin sama a Zamfara, kuma ya buƙaci a gina wajen ajiye jiragen rundunar sojin sama a ciki don ɗaukar matakan gaggawa kan matsalolin tsaro.
“Muna gina filin jirgin sama a Zamfara. Da zarar an kammala, muna fatan samun wajen ajiye jiragen sojin sama a cikinsa domin hanzarta ɗaukar matakan tsaro,” a cewarsa.
Air Marshal Hassan Abubakar ya gode wa gwamnan bisa yadda ya fahimci cewar harin da sojin rundunar suka kai ba da gangan ba ne.
Ya bayyana cewa sojojin sun kai hari ne bisa bayanan sirri kan ayyukan ’yan bindiga, amma daga baya aka gano cewa wasu ’yan sa-kai sun rasa rayukansu a dalilin harin.
Ya tabbatar wa mutanen Zamfara cewa rundunar sojin sama za ta ci gaba da inganta ayyukanta domin kauce wa irin wannan kuskure a nan gaba.