Ofishin watsa labarai na majalissar gudanarwar kasar Sin, ya fitar da wata takardar bayani a baya bayan nan, wadda ta shafi matakan kasar na shawo kan bazuwar sinadarai dangin fentanyl a kasar Sin. 

Yayin taron manema labarai da ya gudana a Juma’ar nan, kakakin ma’aikatar cinikayya ta Sin, ya ce takardar ta fiyyace daukacin matakai, da gabatarwa mai zurfi game da matsayar kasar Sin, da tasirin matakanta na shawo kan bazuwar sinadarai dangin fentanyl ga kasashen duniya.

Gwamna Dauda Ya Rantsar Da Shugaban Ma’aikatan Zamfara Da Sakatarori 12 Xi Ya Yi Kira Da A Kammala Tsare-Tsaren Bunkasa Rundunar Sojin Kasar Sin Na Shekaru 5 Cikin Nasara

Ya ce takardar ta yi cikakken bayani game da yadda Amurka ta kakaba harajin kaso 20 bisa dari kan hajojin kasar Sin da ake shigarwa kasar, ta fakewa da batun sinadarin fentanyl, matakin da ko kadan bai dace ba, kuma mataki ne na kariyar cinikayya, da daukar matsayi na kashin kai da cin zali.

Kasar Sin na kira ga Amurka da ta gyara kurakuren da take tafkawa, ta kuma rika kallon batun wannan sinadari na fentanyl ta mahanga mafi dacewa da sanin ya kamata, ta kuma magance matsalar fentanyl da kan ta, ba tare da dorawa wasu laifi ba. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Trump Yayi Barazanar Karawa China Kashi 50% Na Kudaden Fito A Dai-Dai Lokacinda Suka Shiga Tsakiyar Yakin Tattalin Arziki

Shugaban kasar Amurka Donal Trump yayi barazanar karwa kasar China kasha 50% na kudaden fiton da zata karba daga kayakin kasar China da zasu shiga kasar, idan har bata janye maida martanin da tayi na kasha 34% dai dai karin kudin fito da Amurka ta kara mat aba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a shafinsa na yanar gizo wato ‘Trump Social”.

Kafin haka dai shugaban kasar Amurka ya karawa kasashen duniya da dama wadanda suke huldar kasuwanci da ita kudaden fito na kayakin da suke shigo da su Amurka daga cikin har da kasar China inda Trump ya kara mata kasha 34% na dukkan kayakin China da suke shiga Amurka. Amma kwana guda bayan haka kasar China ta maida martani da kasha 34% na dukkan kayakin Amurka da suke shiga kasar China.

Amma Trump ya bawa kasar China zuwa jiya litinin 8 ga watan Afrilu da muke cikin, na ta janye karin da ta yi wa kayakin Amurka masu shiga China ko kuma ya kara wa kasar ta China kasha 50% kari kan nafarko kan kayakin kasar China masu shigowa Amurka.

Banda yake Trump yace zai dakatar da duk wata tattaunawa da kasar China kan wannan batun. Amma zata bude tattaunawa da sauran kasashen da basu maida martani ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Garin Neman Gira Amurka Za Ta Rasa Ido
  • Kasar Sin Ta Lashi Takobin Sai Ta Ga Abin Da Ya Ture Wa Buzu Nadi Dangane Da Barazanar Haraji Ta Amurka
  • Trump Yayi Barazanar Karawa China Kashi 50% Na Kudaden Fito A Dai-Dai Lokacinda Suka Shiga Tsakiyar Yakin Tattalin Arziki
  • Sharhin Bayan Labarai: Zanga-Zanga A Kasashen Larabawa Ta Goyon Bayan Falasdinaw A Gaza
  • Kasar Sin Ta Nanata Kudurinta Na Ci Gaba Da Bude Kofa Yayin Wani Taro Da Kamfanonin Amurka 
  • Matakin Sin Na Karfafa Takaita Fitar Da Abubuwa Masu Alaka Da Ma’adanan “Rare Rarth” Na Nuni Ga Aniyarta Ta Kare Tsaron Kasa
  • Cin Zali Ba Zai Iya Hana Kasashen Afirka Ci Gaba Ba
  • JMI Ta Kaddamarda Sabbin Ci Gaban Da Ta Samu Da Fasahar Nukliya A Ranar Makamashin Nukliya Ta Kasar
  • Ana Ci Gaba Da Kai Ruwa Rana Takanin Amurka Da China Kan Batun Harajin Fito
  • Amurka ta soke duk wata takardar izinin shiga kasar da aka baiwa ‘yan Sudan ta Kudu