Ofishin watsa labarai na majalissar gudanarwar kasar Sin, ya fitar da wata takardar bayani a baya bayan nan, wadda ta shafi matakan kasar na shawo kan bazuwar sinadarai dangin fentanyl a kasar Sin. 

Yayin taron manema labarai da ya gudana a Juma’ar nan, kakakin ma’aikatar cinikayya ta Sin, ya ce takardar ta fiyyace daukacin matakai, da gabatarwa mai zurfi game da matsayar kasar Sin, da tasirin matakanta na shawo kan bazuwar sinadarai dangin fentanyl ga kasashen duniya.

Gwamna Dauda Ya Rantsar Da Shugaban Ma’aikatan Zamfara Da Sakatarori 12 Xi Ya Yi Kira Da A Kammala Tsare-Tsaren Bunkasa Rundunar Sojin Kasar Sin Na Shekaru 5 Cikin Nasara

Ya ce takardar ta yi cikakken bayani game da yadda Amurka ta kakaba harajin kaso 20 bisa dari kan hajojin kasar Sin da ake shigarwa kasar, ta fakewa da batun sinadarin fentanyl, matakin da ko kadan bai dace ba, kuma mataki ne na kariyar cinikayya, da daukar matsayi na kashin kai da cin zali.

Kasar Sin na kira ga Amurka da ta gyara kurakuren da take tafkawa, ta kuma rika kallon batun wannan sinadari na fentanyl ta mahanga mafi dacewa da sanin ya kamata, ta kuma magance matsalar fentanyl da kan ta, ba tare da dorawa wasu laifi ba. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya Za Ta Karbi Bakuncin Tattaunawar Amurka Da Ukiraniya

Shugaba Zelensky   na Ukiraniya zai kai ziyara kasar Saudiyya a ranar Litinin, gabanin bude tattaunawar da za a yi tsakanin kasarsa da kuma Amurka da zummar kawo karshen yaki da Rasha.

Shugaban na kasar Ukiraniya ya wallafa wani sako a shafinsa na X cewa; Manufar ziyarar tashi ita ce haduwa da yarima mai jiran gado Muhammad Bin Salman, sannan kuma tawagar da zai je da ita, za ta ci gaba da zama a can Saudiyya din saboda yin aiki tare da mutanen Saudiyya da kuma Amurka.”

Zelensky ya kara da cewa; Kasarsa Ukiraniya tana son ganin an sami zaman lafiya mai dorewa.

Bugu da kari shugaban na kasar Ukiraniya ya ce; Matakin farko da kasarsa ta gabatar a matsayin shawarar kai wa ga zaman lafiya, shi ne dakatar da yaki a lokaci mafi kusa, da hakan zai zama share fage ne na warware sabanin da ake da shi baki daya,kuma Ukiraniya a shirye take ta yi aiki da Amurka a turai domin shimfida zaman lafiya”

Dangane da taron da za a yi a kasar Saudiyya, wani babban jami’in gwamnatin kasar ta Ukiraniya ya ce, a ranar Talata mai zuwa za a yi ganawa a tsakanin tawagar kasarsa da kuma ta Amurka a Saudiyya.

Jami’in na Ukiraniya ya ce ganawar za a yi ta ne a kokarin kyautata alaka a tsakanin kasashen biyu, bayan abinda ya faru na cacar baki a tsakanin Donald Trump a Zylenisky.

A gefe daya ministan tsaron Birtaniy John Healey ya furta cewa; Da akwai kyakkyawar dama ta tarihi domin shimfida zaman lafiya a Ukiraniya” sannan ya kara da cewa: “ Shugaban kasar Ukiraniya a shirye yake ya rattaba hannu akan yarjejeniya da Amurka, amma yana da bukatuwa da a ba shi lamuni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taro Na Uku Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin Ya Yi Zama Na Biyu
  • Sin Za Ta Buga Karin Haraji Kan Wasu Hajojin Canada Da Ake Shigarwa Kasar Bayan Kammalar Bincike
  • Saudiyya Za Ta Karbi Bakuncin Tattaunawar Amurka Da Ukiraniya
  • Xi Ya Yi Kira Da A Kammala Tsare-Tsaren Bunkasa Rundunar Sojin Kasar Sin Na Shekaru 5 Cikin Nasara
  • Wang Yi: Diflomasiyyar Kasar Sin Ta Samar Da Kwanciyar Hankalin Da Ake Bukata A Duniya Mai Cike Da Rikici
  • Takun Saka Tsakanin Rasha Da Faransa Kan Batun Kayyade Makaman Nukiliya
  • Nijeriya Za Ta Fara Aiwatar Da Yarjejeniyoyin Haɗin Gwiwa Da Kafofin Watsa Labarai Na Sin – Ministan Yaɗa Labarai
  • Sin Na Maraba Da Jarin Kasa Da Kasa A Fannin Kamfanonin Fasaha
  • Gwamna Namadi Ya Dage Dakatarwar Da Aka Yi Wa Mai Bashi Shawara Na Musamman