Rundunar Tsaro Ta Yi Nasarar Hallaka Wani Jigo Lakurawa A Kebbi
Published: 8th, March 2025 GMT
Rundunar hadaka ta jami’an tsaro da suka hada da ‘yan banga sun yi nasarar hallaka wani kasurgumin jigon kungiyar Lakurawa da aka fi sani da Maigemu a jihar Kebbi.
Sanarwar da Daraktan Tsaron, Alhaji AbdulRahman Usman Zagga, ya fitar, ta ce an kashe Maigemu ne a ranar Alhamis a Kuncin Baba da ke karamar hukumar Arewa, bayan musayar wuta da jami’an tsoro.
Sanarwar ta ce, wannan nasarar ta zo ne mako guda bayan da Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Nasir Idris ya ziyarci al’ummar Bagiza da Rausa Kade a yankin karamar Hukumar Arewa, domin jajantawa al’ummar yankin bisa kashe wasu mutane shida da ake zargin barayin shanun Lakurawa ne suka yi.
An bayyana cewa, matakin da gwamnan jihar ya dauka kan harkokin tsaro ya haifar da d’a mai ido, domin an yi nasarar kashe jagoran Lakurawan, inda aka aje gawarsa a matsayin shaida a asibitin tunawa da Sir Yahaya.
Sanarwar ta ce , daraktan tsaron ya bukaci mazauna yankin da su ba jami’an tsaro hadin kai, ta hanyar sanar da su bayanan sirri da kuma bayar da rahoton abubuwan da ake zargi a yankunansu, domin tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a jihar.
Daga Abdullahi Tukur
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya: An gudanar da zanga-zangar adawa da wasu shirye-shiryen gwamnati
An gudanar da zanga-zangar adawa da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu wada ta barke a wasu manyan biranen Nijeriya da suka haɗa da Abuja da Legas da kuma Fatakwal.
Zanga-zangar wadda wata kungiyar gwagwarmaya ta Take It Back ta shirya na gudana ne duk da gargadin da ’yan sanda suka yi na neman a jingine ta.
A Abuja, babban birnin Nijeriya, fitaccen dan gwagwarmaya, Omoyele Sowore da lauyan nan mai kare hakkin bil Adama, Deji Adeyanju ne ke jagorantar zanga-zangar duk da yunkurin ’yan sanda na hana su rawar gaban hantsi
An kuma hangi masu zanga-zangar ɗauke da alluna da kwalaye masu dauke da rubutun bayyana buƙatunsu a wasu hanyoyi da ke Ikeja, babban birnin Jihar Legas.
A Jihar Ribas kuma, masu zanga-zangar sun yi dandazo a filin Isaac Boro da ke birnin Fatakwal, amma dai ’yan sanda sun rika harba musu barkonon tsohuwa domin daƙile manufar da suka fito ita.
Kungiyar ta Take It Back na cewa babu gudu babu ja da baya domin nuna adawa da dokar ta-baci da aka sanya a Jihar Ribas da kuma abin da ta kira cin zarafin bil’adama da kuma amfani da dokar ta’addancin yanar gizo ba bisa ka’ida ba.
Wannan dai na zuwa ne a yayin da rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta gargaɗi masu shirin zanga-zangar a ranar Litinin 7 ga watan Afrilu a faɗin kasar su sake tunani domin a ranar ce ‘yan sandan kasar suke bukukuwa domin nuna gudunmawar da suka bayar don ci-gaban Nijeriya.
Rundunar ta ce zanga-zangar tana zuwa ne a lokacin da bai dace a yi zanga-zanga a kasar ba.
Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan kasar, Olumuyiwa Adejobi, ya fitar ta ce rundunar ba ta adawa da ‘yancin ‘yan kasar na taruwa da yin gangami da Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya ba su.
Sai dai kuma sanarwar ta ce rundunar na fargaba game da burin wadanda suka shirya yin zanga-zangar rana daya da ranar da aka ware domin yaba wa irin jajircewa da sadaukar da kai na ‘yan sandan Nijeriya.