Rundunar Tsaro Ta Yi Nasarar Hallaka Wani Jigo Lakurawa A Kebbi
Published: 8th, March 2025 GMT
Rundunar hadaka ta jami’an tsaro da suka hada da ‘yan banga sun yi nasarar hallaka wani kasurgumin jigon kungiyar Lakurawa da aka fi sani da Maigemu a jihar Kebbi.
Sanarwar da Daraktan Tsaron, Alhaji AbdulRahman Usman Zagga, ya fitar, ta ce an kashe Maigemu ne a ranar Alhamis a Kuncin Baba da ke karamar hukumar Arewa, bayan musayar wuta da jami’an tsoro.
Sanarwar ta ce, wannan nasarar ta zo ne mako guda bayan da Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Nasir Idris ya ziyarci al’ummar Bagiza da Rausa Kade a yankin karamar Hukumar Arewa, domin jajantawa al’ummar yankin bisa kashe wasu mutane shida da ake zargin barayin shanun Lakurawa ne suka yi.
An bayyana cewa, matakin da gwamnan jihar ya dauka kan harkokin tsaro ya haifar da d’a mai ido, domin an yi nasarar kashe jagoran Lakurawan, inda aka aje gawarsa a matsayin shaida a asibitin tunawa da Sir Yahaya.
Sanarwar ta ce , daraktan tsaron ya bukaci mazauna yankin da su ba jami’an tsaro hadin kai, ta hanyar sanar da su bayanan sirri da kuma bayar da rahoton abubuwan da ake zargi a yankunansu, domin tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a jihar.
Daga Abdullahi Tukur
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Raya Arewa maso Yamma Ta Kai Ziyara Jihar Jigawa
Gwamnatin jihar Jigawa ta ja hankalin shugabannin Hukumar Raya Arewa Maso Yamma da su yi aiki bisa gaskiya da rikon amana domin samun goyon bayan gwamnonin shiyyar.
Gwamna Umar Namadi ya yi kiran ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin hukumar karkashin jagorancin shugabanta Alhaji Lawal Sama’ila Yakawada a gidan gwamnati da ke Dutse.
Ya ce, Hukumar Raya Arewa maso Yamma, ita ce mafi girma a cikin shiyyoyin kasar nan, a don haka bai kamata a fuskanci wasu matsaloli ba daga gareta.
Namadi ya bukace su da su mai da hankali da jajircewa, tare da yin aiki da abubuwan da gwamnoni suka sa gaba domin samun nasara.
Tun da farko, Shugaban Hukumar, Alhaji Lawal Sama’ila Yakawada ya ce sun je ziyarar ce da nufin gabatar da kansu a hukumance da kuma neman tallafi da karfafa gwiwar gwamnati.
A cewarsa, an kafa hukumar ne da amincewar gwamnonin yankin, don haka ya zama wajibi a nemi goyon bayansu.
“Jihar Jigawa jiha cceda ke noma tare da jajircewa, don haka mun ga ya dace mu fara zuwa nan bayan mun ziyarci shugaban kungiyar gwamnonin Arewa, domin samun goyon baya,” in ji Samaila
Alhaji Sama’ila Yakawada ya ce tuni hukumar ta samu bayanai kan bangarorin hadin gwiwa da jihar Jigawa domin bunkasa tattalin arziki da zamantakewa.
Ya bayyana Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yamma a matsayin hukumar da ta fi kowacce hukuma a sauran ayyuka da jihohi bakwai, inda ya ce akwai kalubale da dama.
Shugaban, ya yabawa Gwamna Umar Namadi, bisa kokarinsa na yakar matsalolin da suka addabi al’umma, tun kafin ya hau kujerar gwamnan jihar Jigawa, kamar yadda bayanai suka nuna.
Usman Muhammad Zaria