A cikin abubuwan da aka tattauna a taron, a cikin kananan hukumomi 774, Jihar Delta ce kadai mai kananan hukumomi 25, suka mika bayanan asusunsu domin biyansu kai tsaye.

“Kawo yanzu kananan hukumomin Jihar Delta ne kawai suka bayar da bayanan asusunsu.

“Duk da haka, ana ci gaba da tuntubar babban lauyan gwamnatin tarayya game da yadda ake gabatar da asusun.

Da take maida jawabi kan kalubalen, Madein ta ce an tsara tsarin da za a aiwatar, amma kalubalen farko shi ne na tantance shugabannin kananan hukumomin da tsarin mulki ya zaba.

Ta bayyana cewa wannan matakin ya kasance mara tabbas.

“Bugu da kari, ga wadanda ke da zababben shugabanci, akwai alaman tambaya cewa wasu hanyoyin za a bi don tabbatar da cewa sun sami kasosu kai tsaye. Wannan ya faru ne saboda abubuwa da yawa na bukatar a magance su,” in ji ta.

Idan za a iya tunawa dai, Babban Bankin Nijeriya ya fara bayyana shugabanni da masu sa hannun a asusun bankuna na kananan hukumomi 774 da ke kasar a wani mataki na fara cin gashin kan kananan hukumomi.

Daraktan kula da harkokin shari’a na Babban Bankin Nijeriya, Kofo Salam-Alada, a cikin wata sanarwa ya bayyana cewa hakan ya zama dole domin tabbatar da bin diddigin kudade.

“Wannan duk na cikin tsari sanin abokin hulda. Duk wanda zai zama mai sa hannu a asusun dole ne a bayyana shi.

“Tsarin yana ci gaba, kuma muna hadin gwiwa da ofishin akanta janar. Mun kuma rubuta wa kananan hukumomin,” inj i shi.

Sai dai kungiyar shugabnnin kananan hukumomin Nijeriya ta ce ba ta samu wata sanarwa daga babban bankin kasar ba dangane da bude asusun ajiyar banki.

Idan za a iya tunawa, a ranar 11 ga Yuli, 2024, Kotun Koli ta tabbatar da ikon cin gashin kananan hukumomi 774 da ke kasar nan tare da haramta wa gwamnoni ci gaba da kula da kudaden da aka ware wa kananan hukumomi.

Kotun kolin ta kuma umurci Akanta Janar na Tarayya da ta biya kudaden kananan hukumomi kai tsaye zuwa asusunsu, inda ta bayyana rashin fitar da kudaden da jihohi 36 suka yi ya saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Amma watanni takwas bayan yanke hukuncin, har yanzu ba a fara aiki da hukuncin cin gashin kan kananan hukumomi ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnati Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Sharhin Bayan Labarai: Amurka Ba Zata Taba Zama Mai Kawo Karshin Yaki A Gaza Ba

Assalamu alaikum masu sauraro, sharhin bayan labarammu nay au zai yi magana kan cewa “Amurka ba zata taba zama mai sulhuntawa tsakanin HKI da Falasdinawa ba” wanda ni tahir amin zan karanta.

A dai dai lokacinda rikicin gaza ya zama matsalar ta duniya a halin yanzu, da dama daga cikin masana suna ganin gwamnatin Amurka wacce ta kasance mai goyon bayan HKI na asali ba zata kuma zama mai shiga tsakanin don kawo karshen rikicinta da falasdinawa ba.

Dangane da wannan shafin yanar gizo mai suna “Alkhanadik’ ya rubuta wani sharhi dangane da yakin na gaza a jiya Asabar yana cewa, a dai dai lokacinda gwamnatin kasar Amurka ta kasance bangare babba a cikin haddasa matsaloli ga al-ummar Falasdinu na lokaci mai tsawo , ba zata kuma, zama a lokaci guda mai shiga tsakani don warware wannan matsalar wacce ta zama rikicin kasa da kasa ba.

Saboda ko way a san cewa wanda ya soma yaki ba zai zama mai kuma shiga tsakanin don samar da zaman lafiya ba.

Hakama kamfanin dillancin labaran ISNA na JMI ya nakalto cewa Donal Trump shugaban kasar Amurka yana son ya zama mai sulhuntawa tsakanin HKI da kuma falasdinawa, a rigimar da aka dauki shekaru fiye da 70 ana yenta, kuma gwamnatocin Amurka da suka shude har zuwa yau suna goyon bayan HKI, idan ba ma gwamnatin Amurka ba, da a halin yanzu babu HKI.

Masana sun kara da cewa gaskiyar al-amarin ita ce, a duk lokacinda Amurka da HKI sun yi maganan sulhuntawa ko kuma magance matsalar falasdinawa to kuwa, sai dai su kara rikita al-amarin Falasdinawa ta wani bangaren ne amma ba zasu taba gyara ba.

Don haka abinda muke gani a halin yanzu, ba bambancin sa da abubuwan da suka faru a baya ba, na tattaunawa a lokacinda ake ruwan wuta a kanku.

HKI tana kisan kiyashi a gaza, tana kuma ci gaba da rusa gidajensu da kuma duk wani gina a gaza, suna kashesu ta hanyar sasu yunwa, duniya tana gani, amma kuma a can washintong wasu suna maganar wai ana kokarin ganin yadda za’a kawo karshen rikicin.

Wannan ba sabon abu bane, an sha yin haka a baya. Na farko a samar da matsaloli sannan a yi amfani da shi, don tursasawa bangaren da ke da rauni don karban sharuddan da suka tsara.

Tun cikin watan Octoban shekara ta 2023 HKI tare da cikekken goyon bayan gwamnatin Amurka ta fara kissan kiyashi a Gaza, inda mafi yawan wadanda ake kashewar mata da yara ne, da kuma sunan kare kanta take wannan kissan. Manufarsu a wannan yakin a fili yake, wanda kuma shi ne share zirin gaza daga Falasdinawa. Don haka labaran da suke fitowa daga washinton a cikin yan kwanakin da suka gabata na cewa tana kokarin ganin an warware matsalar Falasdinawa da HKI, wata dasisa ce ta shirin neman wata kasa ko kuma wurin da zasu kwashi falasdinawa a Gaza, su kaisu can, sannan HKI ta shari zirin na Gaza ta ginawa yahudawan da take kwasowa daga kasashen yamma zuwa yankin gidana zama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Yi Allawadai Da Gwamnatin Falasdinawa Kan Masu Goyon Bayanta A Yankin Yamma Da Kogin Jordan
  • Dole Dukkanin Masu Umrah Su Fice Daga Saudiyya Kafin 29 Ga Afrilu – Hukumomi
  • Saudiyya ta musanta hana ’yan Nijeriya biza
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Rika Bayar Da Maganin Hawan Jini Da Siga Kyauta
  • Gaza : adadin ‘yan jaridar da aka kashe ya haura 210
  • Hassan Fadlallah: Amurka ke da alhakin ayyukan wuce gona da iri na Isr’aila a Lebanon
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Kananan Cibiyoyin Kiwon Lafiya 8,880 A Duka Fadin Kasar
  • Burtaniya Ta Soki Gwamnatin Netanyahu Kan Hana ‘Yan Majalisarta Biyu Shiga Cikin Isra’ila
  • Rashin ɗa’a: Gwamnatin Borno ta gargaɗi masu amfani da shafukan sada zumunta
  • Sharhin Bayan Labarai: Amurka Ba Zata Taba Zama Mai Kawo Karshin Yaki A Gaza Ba