A cikin abubuwan da aka tattauna a taron, a cikin kananan hukumomi 774, Jihar Delta ce kadai mai kananan hukumomi 25, suka mika bayanan asusunsu domin biyansu kai tsaye.

“Kawo yanzu kananan hukumomin Jihar Delta ne kawai suka bayar da bayanan asusunsu.

“Duk da haka, ana ci gaba da tuntubar babban lauyan gwamnatin tarayya game da yadda ake gabatar da asusun.

Da take maida jawabi kan kalubalen, Madein ta ce an tsara tsarin da za a aiwatar, amma kalubalen farko shi ne na tantance shugabannin kananan hukumomin da tsarin mulki ya zaba.

Ta bayyana cewa wannan matakin ya kasance mara tabbas.

“Bugu da kari, ga wadanda ke da zababben shugabanci, akwai alaman tambaya cewa wasu hanyoyin za a bi don tabbatar da cewa sun sami kasosu kai tsaye. Wannan ya faru ne saboda abubuwa da yawa na bukatar a magance su,” in ji ta.

Idan za a iya tunawa dai, Babban Bankin Nijeriya ya fara bayyana shugabanni da masu sa hannun a asusun bankuna na kananan hukumomi 774 da ke kasar a wani mataki na fara cin gashin kan kananan hukumomi.

Daraktan kula da harkokin shari’a na Babban Bankin Nijeriya, Kofo Salam-Alada, a cikin wata sanarwa ya bayyana cewa hakan ya zama dole domin tabbatar da bin diddigin kudade.

“Wannan duk na cikin tsari sanin abokin hulda. Duk wanda zai zama mai sa hannu a asusun dole ne a bayyana shi.

“Tsarin yana ci gaba, kuma muna hadin gwiwa da ofishin akanta janar. Mun kuma rubuta wa kananan hukumomin,” inj i shi.

Sai dai kungiyar shugabnnin kananan hukumomin Nijeriya ta ce ba ta samu wata sanarwa daga babban bankin kasar ba dangane da bude asusun ajiyar banki.

Idan za a iya tunawa, a ranar 11 ga Yuli, 2024, Kotun Koli ta tabbatar da ikon cin gashin kananan hukumomi 774 da ke kasar nan tare da haramta wa gwamnoni ci gaba da kula da kudaden da aka ware wa kananan hukumomi.

Kotun kolin ta kuma umurci Akanta Janar na Tarayya da ta biya kudaden kananan hukumomi kai tsaye zuwa asusunsu, inda ta bayyana rashin fitar da kudaden da jihohi 36 suka yi ya saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Amma watanni takwas bayan yanke hukuncin, har yanzu ba a fara aiki da hukuncin cin gashin kan kananan hukumomi ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gwamnati Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Mamaya Sun Yi Kasan Kiyashi A Zirin Gaza Da Kuma Ci Gaba Da Killace Falasdina  Cikin Masifar Yunwa

Sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da kashe-kashen kisan kiyashi, kuma ana ci gaba da fama da yunwa a Gaza a daidai lokacin da kasashen duniya suka yi shiru

An shiga rana ta arba’in da fara sabon farmakin da haramtacciyar kasar Isra’ila ke kai wa Zirin Gaza, a daidai lokacin da ake ci gaba da samun ta’adi da kisan kare dangi da ba a taba ganin irinsa ba, a daidai lokacin da Amurka ke goyon bayan ta’asar da kuma shiru na kasa da kasa wanda masu lura da al’amura suka bayyana a matsayin babban abin kunya.

A cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza, adadin wadanda suka yi shahada  sakamakon hare-haren ta’addancin ‘yan sahayoniyya ya kai 51,355 da kuma jikkatan wasu 117,248 tun daga ranar 7 ga watan Oktoban shekara ta 2023.

Adadin wadanda suka yi shahada da jikkata tun daga ranar 18 ga watan Maris na wannan shekara ta 2025, watau kwanaki arba’in, ya kai kimanin shahidai 2,000 da kuma jikkatan 5,207.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Falasdinawa 39 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’o’I 24
  • Iran ta Bayyana cewa: TattaunawarMuscat Wata Dama Ce Ta Samun Zaman Lafiya Kan Batutuwan Masu Sarkakiya
  • Sojojin Mamaya Sun Yi Kasan Kiyashi A Zirin Gaza Da Kuma Ci Gaba Da Killace Falasdina  Cikin Masifar Yunwa
  • Gwamnan Babban Bankin Sin: Harajin Amurka Ya Jefa Kasuwanni Da Kasashe Masu Tasowa Cikin Hadari
  • An Gano Naira Miliyan 27.8 Da Suke Zirarewa A Albashin Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Gano  An Biya Wasu Ma’aikatan Bogi Naira Miliyoyi
  • Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya