Ya bayyana cewa samun damar karɓar baƙuncin wannan babban taro wata gagarumar nasara ce ga Nijeriya, kasancewar ita ce ƙasar Afirka ta biyu da za ta karɓi baƙuncin taron.

 

Ya ce: “Wannan babban cigaba ne ga Nijeriya kuma yana da alaƙa da manufofin gwamnatin mu na inganta martabar ƙasar a idon duniya.

A daidai lokacin da muke aiwatar da muhimman sauye-sauye da ƙarfafa matsayar mu a duniya, karɓar baƙuncin WPRF wata alama ce cewa duniya tana kallon Nijeriya.

 

“Gwamnati za ta bayar da cikakken goyon baya don tabbatar da nasarar wannan taro.”

 

Ya kuma bayyana wata muhimmiyar nasara, inda ya ce Nijeriya ta samu damar karɓar baƙuncin Cibiyar UNESCO ta Mataki na Biyu kan Ilimin Kafofin Watsa Labarai da Bayani (MIL), wadda ita ce irin ta ta farko a Afrika.

 

Ya ce wannan matakin yana nuna irin girman tasirin da Nijeriya take samu a duniya.

 

Ya ce: “Hulɗa da jama’a tana da muhimmiyar rawa wajen gina ƙasa, bunƙasa dimokiraɗiyya, da inganta martabar Nijeriya a duniya.

 

“Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai tana da ecikakken niyyar yin aiki tare da duk masu ruwa da tsaki domin cimma wannan buri da kuma ba Nijeriya matsayi na jagora a fagen sadarwa na duniya.”

 

A nasa jawabin, Shugaban NIPR, Dakta Ike Neliaku, ya yaba wa ministan bisa ƙwazon da yake yi wajen inganta sarrafa bayanai da hulɗa da jama’a a ƙasar.

 

Ya ce: “Yanzu muna kallon sarrafa bayanai a matsayin hanyar sadarwa ta ɓangarori biyu, wato inda muke karɓar ra’ayoyi daga jama’a don su taimaka mana wajen tsara matakai na gaba.”

 

Dakta Neliaku ya kuma ba da sanarwar cewa Nijeriya za ta karɓi baƙuncin bikin cika shekaru 25 na ƙungiyar Global Alliance a shekarar 2026, wanda hakan zai ƙara tabbatar da matsayin ƙasar a matsayin jagaba a fagen hulɗa da jama’a a duniya.

 

Bugu da ƙari, ya sanar da ministan manyan shirye-shiryen da NIPR ta tsara na shekarar 2025, wanda suka haɗa da Makon Hulɗa da Jama’a na Nijeriya (NPR Week), Taron Ƙasa na Masu Magana da Yawu, da Taron Ƙasa kan Sarrafa Sunan Nijeriya.

 

Tawagar shugabannin NIPR ɗin ta haɗa da Mataimakin Shugaba, Farfesa Emmanuel Dandaura, da wasu manyan jami’ai, ciki har da Cif Yomi Badejo-Okusanya, Mohammed Kudu Abubakar, da Cif Uzoma Onyegbadue.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: karɓar baƙuncin

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Fadada Bude Kofar Kasar Sin Ke Haifar Da Damammaki Ga Duniya

Yayin da tattalin arzikin kasar Sin ke kara samun tagomashi, masana daga sassa daban daban, na ganin hakan dama ce ta ci gaban duniya baki daya. Kamar dai yadda sakamakon wani bincike, na asusun ba da lamuni na duniya IMF ya nuna yadda bunkasar tattalin arzikin kasar Sin ke shafar ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya. Binciken ya nuna bunkasar tattalin arzikin Sin da karin kaso daya bisa dari, yake haifar da matsakaicin bunkasar tattalin arzikin sauran sassan kasa da kasa da kaso 0.3 bisa dari.

Duba da haka, ma iya cewa duniya za ta ci gaba da shan romon bunkasar tattalin arzikin kasar Sin, yayin da kasar ke ta kara fadada manufofinta na bude kofa ga sassan duniya. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • WHO Za Ta Bai Wa Najeriya Magungunan Cutar Kuturta
  • Nijeriya Za Ta Nuna Gyare-gyaren Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu A Taron Kasuwanci A Faransa
  • WHO za ta bai wa Nijeriya magungunan cutar kuturta
  • Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Da CGTN Ta Gudanar Ya Shaida Gamsuwar Al’ummun Duniya Da Salon Diflomasiyyar Sin
  • FUD Ta Nada Abdullahi Yahaya Bello Daraktan Hulda da Jama’a
  • Wang Yi: Diflomasiyyar Kasar Sin Ta Samar Da Kwanciyar Hankalin Da Ake Bukata A Duniya Mai Cike Da Rikici
  • Burin Gwamnatin Sin Na Bunkasa Gdp Da Kashi 5% A Bana Ya Bayyana Niyyarta Ta Samun Ingantaccen Ci Gaban Tattalin Arziki
  • Shugaban NAN:Muna Iya Ganin Basirar Sin Ta Manyan Taruka Biyu Da Take Gudanarwa Yanzu
  • Yadda Fadada Bude Kofar Kasar Sin Ke Haifar Da Damammaki Ga Duniya