Ya bayyana cewa samun damar karɓar baƙuncin wannan babban taro wata gagarumar nasara ce ga Nijeriya, kasancewar ita ce ƙasar Afirka ta biyu da za ta karɓi baƙuncin taron.

 

Ya ce: “Wannan babban cigaba ne ga Nijeriya kuma yana da alaƙa da manufofin gwamnatin mu na inganta martabar ƙasar a idon duniya.

A daidai lokacin da muke aiwatar da muhimman sauye-sauye da ƙarfafa matsayar mu a duniya, karɓar baƙuncin WPRF wata alama ce cewa duniya tana kallon Nijeriya.

 

“Gwamnati za ta bayar da cikakken goyon baya don tabbatar da nasarar wannan taro.”

 

Ya kuma bayyana wata muhimmiyar nasara, inda ya ce Nijeriya ta samu damar karɓar baƙuncin Cibiyar UNESCO ta Mataki na Biyu kan Ilimin Kafofin Watsa Labarai da Bayani (MIL), wadda ita ce irin ta ta farko a Afrika.

 

Ya ce wannan matakin yana nuna irin girman tasirin da Nijeriya take samu a duniya.

 

Ya ce: “Hulɗa da jama’a tana da muhimmiyar rawa wajen gina ƙasa, bunƙasa dimokiraɗiyya, da inganta martabar Nijeriya a duniya.

 

“Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai tana da ecikakken niyyar yin aiki tare da duk masu ruwa da tsaki domin cimma wannan buri da kuma ba Nijeriya matsayi na jagora a fagen sadarwa na duniya.”

 

A nasa jawabin, Shugaban NIPR, Dakta Ike Neliaku, ya yaba wa ministan bisa ƙwazon da yake yi wajen inganta sarrafa bayanai da hulɗa da jama’a a ƙasar.

 

Ya ce: “Yanzu muna kallon sarrafa bayanai a matsayin hanyar sadarwa ta ɓangarori biyu, wato inda muke karɓar ra’ayoyi daga jama’a don su taimaka mana wajen tsara matakai na gaba.”

 

Dakta Neliaku ya kuma ba da sanarwar cewa Nijeriya za ta karɓi baƙuncin bikin cika shekaru 25 na ƙungiyar Global Alliance a shekarar 2026, wanda hakan zai ƙara tabbatar da matsayin ƙasar a matsayin jagaba a fagen hulɗa da jama’a a duniya.

 

Bugu da ƙari, ya sanar da ministan manyan shirye-shiryen da NIPR ta tsara na shekarar 2025, wanda suka haɗa da Makon Hulɗa da Jama’a na Nijeriya (NPR Week), Taron Ƙasa na Masu Magana da Yawu, da Taron Ƙasa kan Sarrafa Sunan Nijeriya.

 

Tawagar shugabannin NIPR ɗin ta haɗa da Mataimakin Shugaba, Farfesa Emmanuel Dandaura, da wasu manyan jami’ai, ciki har da Cif Yomi Badejo-Okusanya, Mohammed Kudu Abubakar, da Cif Uzoma Onyegbadue.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: karɓar baƙuncin

এছাড়াও পড়ুন:

An Fara Gudanar Da Zaman Taron Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Tsakanin Iran Da Kasashen Nahiyar Afirka

An fara gudanar da zaman taron hadin gwiwar tattalin arziki tsakanin  Iran da kasashen nahiyar Afirka karo na uku

A safiyar yau Lahadi ne aka bude zaman taron karo na uku kan harkokin tattalin arziki tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kasashen Afirka a birnin Tehran, tare da halartar shugaban kasar Iran da mataimakinsa na farko da wasu tawagar jami’ai da ‘yan kasuwa daga nahiyar Afirka.

Kasar Iran tana gudanar da wannan biki ne tare da jami’an kungiyar Tarayyar Afirka, da manyan jami’ai, ministocin tattalin arziki da cinikayya, da shugabannin kungiyoyin kasuwanci, ‘yan kasuwa, masu fafutukar tattalin arziki, shugabannin bankuna, kamfanonin inshora, da na’urorin samar da kayayyaki, da daraktocin manyan kamfanoni da na kasa da kasa daga kasashen Afirka.

Taron hadin gwiwar tattalin arziki na Iran da Afirka na wakiltar wani sauyi a tsarin Iran na samar da hadin gwiwa da kasashen nahiyar ta Afirka. A Juyin lokaci a cikin hanyoyin haɗin gwiwa, nahiyar Afirka tana wakiltar wata dama ta musamman ga kasashe masu tasowa ta hanyar kasuwanci. Kasashen Afirka na bukatar su shigo da kayayyaki, da ayyuka, da kwararrun ma’aikata domin shawo kan koma bayan da suka fuskanta a tarihi, kuma Iran da alama tana iyaka kokarinta na taimakawa kasashen Afirka a wannan fanni.

A ranar Litinin ne ‘yan kasuwar za su ziyarci baje kolin Iran, kuma a ranar Talata bayan kammala wani taron karawa juna sani a zauren taron koli na tekun Fasha, za su nufi birnin Isfahan, tare da rakiyar tawagogin gwamnati da ‘yan kasuwar Afirka, inda za su gudanar da taruka na musamman da kuma ziyartar cibiyoyi da masana’antu fiye da 10 a lardin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
  • Fira Ministan Indiya Ya Bayyana Cewa: Iran Tana Kokari A Fagen Inganta Zaman Lafiya A Yanki Da Duniya Baki Daya
  • An Fara Gudanar Da Zaman Taron Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Tsakanin Iran Da Kasashen Nahiyar Afirka
  • Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje
  • Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’
  • An Gudanar Da Dandalin Kirkire-kirkire Na Kafofin Watsa Labarai Na Duniya Karo Na 4 A Birnin Qufu Na Kasar Sin