Aminiya:
2025-03-09@12:04:30 GMT

An kashe shugaban Lakurawa, Maigemu a Kebbi

Published: 8th, March 2025 GMT

Jami’an tsaro da ’yan sa-kai sun kashe shugaban ’yan ta’addan Lakurawa, Maigemu, a Jihar Kebbi.

Daraktan Tsaro na Jihar Kebbi, AbdulRahman Usman Zagga ne, ya shaida wa manema labarai a ranar Juma’a cewa an kashe Maigemu a ranar Alhamis.

PDP ta soki dakatar da Natasha, ta nemi a binciki Akpabio Fashewar tankar mai: Mutum 7 sun mutu, gonaki sun lalace a Neja

Ya ce an kashe shi ne yayin musayar wuta da jami’an tsaro a garin Kuncin Baba da ke Ƙaramar Hukumar Arewa.

Mutuwarsa ta zo ne mako guda bayan da Gwamna Nasir Idris ya kai ziyarar jaje ƙauyukan Bagiza da Rausa Kade, inda ’yan ta’adda suka kashe mutum shida.

“Ƙoƙarin gwamna ya haifar da ɗa mai ido, domin yanzu an kashe wannan babban shugaban ’yan ta’adda. Gawarsa tana nan a matsayin shaida,” in ji Zagga.

Ya yaba wa gwamnan bisa ƙoƙarinsa na tabbatar da tsaro da kuma tallafin da yake bai wa jami’an tsaro a kai a kai.

Zagga ya kuma roƙi jama’a da su ci gaba da haɗa kai da jami’an tsaro ta hanyar ba su bayanai da kuma kai rahoton duk wani abun zargi domin samar da zaman lafiya mai ɗorewa a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami an Tsaro Lakurawa musayar wuta

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Raya Arewa maso Yamma Ta Kai Ziyara Jihar Jigawa

Gwamnatin jihar Jigawa ta ja hankalin shugabannin Hukumar Raya Arewa Maso Yamma  da su yi aiki bisa gaskiya da rikon amana domin samun goyon bayan gwamnonin shiyyar.

Gwamna Umar Namadi ya yi kiran ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin hukumar karkashin jagorancin shugabanta Alhaji Lawal Sama’ila Yakawada a gidan gwamnati da ke Dutse.

Ya ce, Hukumar Raya Arewa maso Yamma, ita ce mafi girma a cikin shiyyoyin kasar nan, a don haka bai kamata a fuskanci wasu matsaloli  ba daga gareta.

Namadi ya bukace su da su mai da hankali da jajircewa, tare da yin aiki da abubuwan da gwamnoni suka sa gaba domin samun nasara.

Tun da farko, Shugaban Hukumar, Alhaji Lawal Sama’ila Yakawada ya ce sun je ziyarar ce da nufin gabatar da kansu a hukumance da kuma neman tallafi da karfafa gwiwar gwamnati.

A cewarsa, an kafa hukumar ne da amincewar gwamnonin yankin, don haka ya zama wajibi a nemi goyon bayansu.

“Jihar Jigawa jiha cceda ke noma tare da jajircewa, don haka mun ga ya dace mu fara zuwa nan bayan mun ziyarci shugaban kungiyar gwamnonin Arewa, domin samun goyon baya,” in ji Samaila

Alhaji Sama’ila Yakawada ya ce tuni hukumar ta samu bayanai kan bangarorin hadin gwiwa da jihar Jigawa domin bunkasa tattalin arziki da zamantakewa.

Ya bayyana Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yamma a matsayin hukumar da ta fi kowacce hukuma a sauran ayyuka da jihohi bakwai, inda ya ce akwai kalubale da dama.

Shugaban, ya yabawa Gwamna Umar Namadi, bisa kokarinsa na yakar matsalolin da suka addabi al’umma, tun kafin ya hau kujerar gwamnan jihar Jigawa, kamar yadda  bayanai suka nuna.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An harbe shugaban ƙungiyar Miyetti Allah a Kwara
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Jega Mai Ba Shi Shawara Na Musamman Kan Harkokin Kiwon Dabbobi
  • Hukumar Raya Arewa maso Yamma Ta Kai Ziyara Jihar Jigawa
  • Rundunar Tsaro Ta Yi Nasarar Hallaka Wani Jigo Lakurawa A Kebbi
  • Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
  • Kisan malami: Shugabannin Kiristocin Kudancin Kaduna sun yi Allah-wadai
  • Ƙasurmugin Ɗan Ta’adda Maigemu Ya Shiga Hannu A Kebbi
  • Gwamnatin Kebbi Ta Sha Alwashin Kawar Da Matsalar Abinci A Jihar
  • Jami’an NDLEA Sun Kashe Budurwa A Kano, An Damƙe Su