Aminiya:
2025-04-09@00:03:42 GMT

An kashe shugaban Lakurawa, Maigemu a Kebbi

Published: 8th, March 2025 GMT

Jami’an tsaro da ’yan sa-kai sun kashe shugaban ’yan ta’addan Lakurawa, Maigemu, a Jihar Kebbi.

Daraktan Tsaro na Jihar Kebbi, AbdulRahman Usman Zagga ne, ya shaida wa manema labarai a ranar Juma’a cewa an kashe Maigemu a ranar Alhamis.

PDP ta soki dakatar da Natasha, ta nemi a binciki Akpabio Fashewar tankar mai: Mutum 7 sun mutu, gonaki sun lalace a Neja

Ya ce an kashe shi ne yayin musayar wuta da jami’an tsaro a garin Kuncin Baba da ke Ƙaramar Hukumar Arewa.

Mutuwarsa ta zo ne mako guda bayan da Gwamna Nasir Idris ya kai ziyarar jaje ƙauyukan Bagiza da Rausa Kade, inda ’yan ta’adda suka kashe mutum shida.

“Ƙoƙarin gwamna ya haifar da ɗa mai ido, domin yanzu an kashe wannan babban shugaban ’yan ta’adda. Gawarsa tana nan a matsayin shaida,” in ji Zagga.

Ya yaba wa gwamnan bisa ƙoƙarinsa na tabbatar da tsaro da kuma tallafin da yake bai wa jami’an tsaro a kai a kai.

Zagga ya kuma roƙi jama’a da su ci gaba da haɗa kai da jami’an tsaro ta hanyar ba su bayanai da kuma kai rahoton duk wani abun zargi domin samar da zaman lafiya mai ɗorewa a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami an Tsaro Lakurawa musayar wuta

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta kona motoci 10 a garejin Borno Express

Wata gobara da ta ɓarke ta cinye garejin gyaran motocin kamfanin sufurin Borno Express na Gwamnatin Jihar Borno, inda ta lalata motocin bas sama da 10 masu daukar mutane 18 kowacce.

Shaidu sun ce gobarar ta fara ne da misalin ƙarfe 12 na rana a ranar Litinin, bayan wani fashewa mai ƙarfi a harabar garejin.

Ko da yake babu wanda ya rasa ransa a wannan lamarin, wani ma’aikacin hukumar kashe gobara ya samu raunuka yayin da yake kokarin kashe gobarar.

Wani ganau ya ce, “Gobarar ta tashi ne sakamakon fashewar tukunyar gas — inda wani kara mai ban tsoro ya sa ma’aikata da matafiya a yankin suka yi ta gujegujen domin tsira.”

Gobara ta laƙume ƙauyuka a Borno Mahara sun yi garkuwa da fiye da mutum 50 a Katsina Kisan Janar Alƙali: Kotu ta ɗage shari’a zuwa 28 ga Mayu

Ya ƙara da cewa, “Hanzarin da hukumar kashe gobara ta yi ne ya hana lamarin ƙara ƙazancewa. Sun isa da sauri kuma sun yi nasarar shawo kan gobarar.”

Kwamishinan Sufuri da Makamashi na Jihar Borno, Aliyu Buba Bamanga, ya ziyarci wurin da lamarin ya faru amma ya ƙi yin tsokaci.

Kwamishinan ya ce, “Muna jiran Mai Girma Gwamna Babagana Umara Zulum nan ba da jimawa ba. Ba zan so yin magana kafin wata sanarwa ta hukuma daga gare shi ba.”

Wani ma’aikacin garejin ya shaida wa wakilinmu cewa galibin motocin da abin ya shafa motocin bas ne masu ɗaukar mutane 18 da ake yi wa gyaran yau da kullum, da kuma wasu ƙalilan da ake yi musu manyan gyare-gyare.

“Mun auna arziki  da gobarar ba ta shafi wurin cajin motocin lantarki da ke kusa ba, da gobarar ta kai can, da munin lamarin ya ɓaci.”

Garejin gyaran motocin, wanda Kamfanin Sufuri na Borno Express ke gudanarwa, yana da alhakin kula da motocin zirga-zirgar jama’a na jihar.

Wannan lamarin ya faru ne kwana daya kacal bayan wata gobara ta cinye dubban gidaje a wasu yankuna huɗu a Alau, Jihar Borno, ind ta yi sanadiyyar mutuwar mutane biyu tare da lalata dukiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kisan Isuhu Yellow: ’Yan bindiga sun kai harin ɗaukar fansa
  • Lakurawa Sun Kashe ’Yan Sa-kai 13 A Wani Sabon Hari A Kebbi
  • Gobara ta kona motoci 10 a garejin Borno Express
  • Matsalar tsaro: Ba za mu lamunci zagon ƙasa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Hatsarin mota ya kashe mutane 5 a Yobe
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 4, Sun Sace 45 A Katsina
  • Lakurawa sun kashe ’yan sa-kai 13 a Kebbi
  • Harin Filato: An kashe Mutane 40, An Kona Gidaje 383, Fiye Da Mutane 1,000 An Raba Su Da Muhallansu 
  • ACF ta nemi Gwamnatin Tarayya ta kawo ƙarshen kisan jama’a a Filato
  • Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya