Gwamnatin tarayya ta nuna damuwarta kan cewa kasar nan ta yi asarar tiriliyoyin naira sakamakon ayyukan masu hakar ma’adanai ta barauniyar hanyoyi musamman a jihohi.

Gwamnatin ta kuma cafke da gurfanar da ‘yan kasan waje su hudu wadanda suka shiga harkar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, yayin da wasu mutane 320 kuma aka cafke kan harkokin satar ma’adinai.

A cewar gwamnatin, cikin wadanda aka kama 320, kusan mutum 150 a halin yanzu suna fuskantar shari’a kuma wasu guda tara an dauresu, inda su kuma mutum hudu ‘yan kasar wajen aka dauresu a gidan yari.

Ministan bunkasa albarkatun kasa, Dele Alake, shi ne ya shaida hakan a lokacin da ke ganawa da manema labarai a karshen zaman majalisar zartarwa na tarayya (FEC) wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta.

Ministan ya kuma ce, gwamnatin tarayya ta fuskanci kalubale wajen shawo kan matsalar hako zinari, musamman a arewacin Nijeriya, saboda al’adu.

Alake ya bayyana cewa majalisar zartarwar ta amince da wani sabon shiri na inganta tsari da kuma dakile asarar kudaden shiga a fannin ma’adinai.

A wani bangare na shirin, ya ce gwamnati za ta tura fasahar tauraron Dan’adam don sa ido kan muhimman wuraren hakar ma’adinai da kuma bin diddigin ayyukan ma’adani.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Dage Dakatarwar Da Aka Yi Wa Mai Bashi Shawara Na Musamman

Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya dage dakatarwar da aka yi wa mai bashi shawara na musamman kan harkokin albashi da fansho, Bashir Ado Kazaure da aka mishi a baya ba tare da bata lokaci ba.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Jigawa Malam Bala Ibrahim ya sanyawa hannu kuma ya bai wa manema labarai.

Sanarwar ta bayyana cewa, matakin na zuwa ne bayan wani kwakkwaran bincike da kwamitin da aka kafa karkashin jagorancin babban lauyan gwamnati kuma kwamishinan shari’a na jihar Barista Bello Abdulkadir Fanini ya gudanar.

“Rahoton kwamitin ya yi tsokaci kan al’amuran da suka dabaibaye dakatarwar da aka yi wa Bashir Kazaure, biyo bayan sanarwar  batun biyan mafi karancin albashi na Naira 70,000 kafin lokacin da gwamnati ta shirya sanarwa a hukumance,” in ji shi.

Sakataren gwamnatin jihar ya bayyana cewa, matakin dage dakatarwar na nuni da yadda Gwamnan ya jajirce wajen tabbatar da adalci da bin doka da oda wajen tafiyar da al’amura.

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ramadan: Imani, Siyasa Dole Su Hadu Don Ci Gaban Kasa – Ministan Yada Labarai
  • Ramadan: Imani da Siyasa Dole Su Hadu Don Ci Gaban Kasa – Ministan Yada Labarai
  • Nijeriya Ta Yi Asarar Tiriliyoyin Naira Kan Hakar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba – Gwamnati
  • An Yi Hada- hadar Dala 1 Kan Naira 1,500 A Kasuwannin Musayar Kudi
  • Yansanda A Najeriya Sun Kama Yan Kasar Pakistan Biyu Da Hakanni Wajen Sake Yan Kasashen Waje A Kasar
  • NAJERIYA A YAU: Falalar Buɗa-baki Cikin Iyali A Lokacin Azumi
  • Gwamnatin Kebbi Ta Sha Alwashin Kawar Da Matsalar Abinci A Jihar
  • Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya Ta Jinjinawa Gwamnatin Jigawa Bisa Wanzar Da Zaman Lafiya
  • Gwamna Namadi Ya Dage Dakatarwar Da Aka Yi Wa Mai Bashi Shawara Na Musamman