Gwamnatin tarayya ta nuna damuwarta kan cewa kasar nan ta yi asarar tiriliyoyin naira sakamakon ayyukan masu hakar ma’adanai ta barauniyar hanyoyi musamman a jihohi.

Gwamnatin ta kuma cafke da gurfanar da ‘yan kasan waje su hudu wadanda suka shiga harkar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, yayin da wasu mutane 320 kuma aka cafke kan harkokin satar ma’adinai.

A cewar gwamnatin, cikin wadanda aka kama 320, kusan mutum 150 a halin yanzu suna fuskantar shari’a kuma wasu guda tara an dauresu, inda su kuma mutum hudu ‘yan kasar wajen aka dauresu a gidan yari.

Ministan bunkasa albarkatun kasa, Dele Alake, shi ne ya shaida hakan a lokacin da ke ganawa da manema labarai a karshen zaman majalisar zartarwa na tarayya (FEC) wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta.

Ministan ya kuma ce, gwamnatin tarayya ta fuskanci kalubale wajen shawo kan matsalar hako zinari, musamman a arewacin Nijeriya, saboda al’adu.

Alake ya bayyana cewa majalisar zartarwar ta amince da wani sabon shiri na inganta tsari da kuma dakile asarar kudaden shiga a fannin ma’adinai.

A wani bangare na shirin, ya ce gwamnati za ta tura fasahar tauraron Dan’adam don sa ido kan muhimman wuraren hakar ma’adinai da kuma bin diddigin ayyukan ma’adani.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Likitocin Nijeriya dubu 16 sun yi ƙaura zuwa ƙetare — Ministan Lafiya

Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Pate ya bayyana cewa, sama da likitoci dubu 16 sun fice daga Nijeriya a cikin shekaru biyar zuwa bakwai da suka gabata zuwa wasu ƙasashen duniya don ci gaba da aiki cikin ingantaccen yanayi.

Farfesa Pate ya bayyana haka ne a wurin taron horas da Ƙungiyar Likitocin Afrika da ya gudana a birnin Abuja a ranar Talata.

Nijar ta ayyana Hausa a matsayin yaren ƙasa DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’

Ministan ya bayyana cewa, ana ci gaba da samun wani adadi mai yawa na ƙwararrun likitocin da ke da burin fita zuwa wasu ƙasashen duniya aiki, suna fakewa da matsalolin tattalin arziƙi da rashin kyawun yanayin aiki da kuma samun cikakken horo, baya ga zurfafa gudanar da bincike a ƙasashen na ƙetare.

Kodayake ya ce, ficewar ƙwararrun likitoci daga ƙananan ƙasashe zuwa ƙasashen da suka ci gaba, ba sabon labari ba ne, amma sai dai adadinsu na ƙara yawaita a shekarun baya-baya nan a cewarsa.

Pate ya kuma bayyana takaicinsa kan yadda su ma nas-nas da unguwarzoma suka fice daga ƙasar, lamarin da ya ƙara zabtare adadin ma’aikatan lafiyar da ake da su a Najeriya.

A cewar Ministan Lafiyar, kididdiga ta nuna kusan likitoci huɗu ne ke duba mutum dubu 10 a ƙasar, yana mai ƙiyasta sama da Dala dubu 21 a matsayin kuɗin da ake kashe wa kowanne likita guda wajen horas da shi.

“A Najeriya kaɗai, sama da likitoci dubu 16 aka ƙiyasta sun fice daga ƙasar a cikin shekaru biyar zuwa bakwai. Nas-nas da unguwarzoma su ma sun yi ƙaranci.

“Yanzu likita kusan huɗu ne ke duba mutum dubu 10, adadin da ya yi ƙasa sosai idan aka kwatanta da alkaluman da aka amince da su a matakin duniya.”

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Likitocin Nijeriya dubu 16 sun yi ƙaura zuwa ƙetare — Ministan Lafiya
  • Zulum: Boko Haram na sake kwace iko da wasu yankuna a Borno
  • Ma’aikatar Jin-ƙai ce kan gaba wajen wawure kuɗin gwamnati — Tsohon Minista
  • ɗin aikatar Jin-ƙai ce kan gaba wajen wawure kudin gwamnati — Tsohon Minista
  • Najeriya: An gudanar da zanga-zangar adawa da wasu shirye-shiryen  gwamnati
  • Matsalar tsaro: Ba za mu lamunci zagon ƙasa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • ACF Ta Bukaci Gwamnatin Najeriya Da Ta Kawo Karshe Tashe-Tashen Hankula Filato
  • ACF ta nemi Gwamnatin Tarayya ta kawo ƙarshen kisan jama’a a Filato
  • Burtaniya Ta Soki Gwamnatin Netanyahu Kan Hana ‘Yan Majalisarta Biyu Shiga Cikin Isra’ila
  • Kanwan Katsina Ya Yabi Gwamnatin Katsina Kan Farfado Da Al’adar Hawan Durbar