Rahotanni da ke fitowa daga kasar suna nuni da cewa, Yawancin fararen hula da aka kashe a tashe-tashen hankulan da suka faru a wannan Juma’a, dakarun sabuwar gwamnatin kasar ta Syria ne suka kashe su, kamar yadda binciken kungiyar kare hakkin bil Adam ta (SOHR) ya tabbatar.

Ayyukan tashe-tashen hankulan sun yi sanadin Kisan mutuwar fararen hula 162 a lardunan gabar tekun Syria, ciki har da mata da kananan yara, in ji rahoton kungiyar ta SOHR.

Akasarin wadanda aka kashe dai kamar yadda aka gani a wasu fayafayin bidiyo da aka dauka, jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria ne da suke da alaka kungiyoyi masu tsatsauran ra’ayi irin su Tahrir Sham da makamantansu da suke da alaka da Alqaida ne suka kama mutanen, bisa tuhumar cewa suna da alaka da tsohuwar gwamnatin Bashar Assad, a kan haka suka yanke musu hukuncin kisa a nan take kuma suka kashe su.

Kungiyar ta ce wannan matakin na nuni da irin mawuyacin hali mai matukar hadari da Syria ta fada a ciki, inda ake ci gaba da cin zarafi  jama’a da kuma muzguna musu da sunan daukar fansa a kan tsiraru marasa rinjaye.

Wasu daga cikin Hotunan da aka dauka sun yadu a shafukan sada zumunta, wadanda suke nuni da manyan laifukan yaki. Rahoton ya ce wasu daga cikin faifan bidiyo sun nuna lokacin da jami’an tsaron sabuwar  suka harbe wasu ‘yan kasar Syria da ba su dauke da makami, wadanda aka wulakanta su kafin a yi musu kisan gilla.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ta Gano  An Biya Wasu Ma’aikatan Bogi Naira Miliyoyi

Gwamnatin Jihar Kano ta gano matsaloli a cikin tsarin albashin ma’aikatan ƙananan hukumomi, inda aka gano ma’aikata 247 da suka yi ritaya ko kuma sun mutu, amma suna ci gaba da karɓar albashi.

Wannan bayani ya fito ne daga cikin wata sanarwa da mataimakin shugaban ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Musa Muhammad, ya fitar. A cewar sanarwar, wannan bincike ya gudana ne a yayin da ake gudanar da aikin tantancewa domin gyara tsarin albashin ma’aikatan gwamnati a jihar.

Har Yanzu Da Akwai Jihohin Da Malaman Makaranta Ke Karbar Albashin Naira 18,000 NLC Ta Yi Zanga-Zanga A Ofishin Wike, Ta Nemi A Biya Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi Albashin N70,000

Sanarwar ta bayyana cewa, duk da cewa waɗannan ma’aikatan sun yi ritaya ko kuma sun mutu, sun kasance suna cikin jerin sunayen ma’aikatan da ke karɓar albashi, wanda hakan ya kai ga biyan kuɗi na ƙarya har Naira miliyan 27,824,395.40 a watan Maris na shekarar 2025 kawai.

Gwamnatin Kano ta tabbatar da cewa an dawo da wannan kuɗi zuwa asusun ƙananan hukumomi, kuma za a ci gaba da bincike don gano duk wanda ya yi wannan zamba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar
  • An kashe sojoji 12 a barikin Nijar
  •  Nigeria: Boko Haram Ta Kashe Mutane 12 A Borno
  •  Dakarun Kai Daukin Gaggawa Na Sudan Sun kashe ‘Yan Hijira Da Dama A Yankin Tekun Maliya
  •  Adadin Wadanda Su ka Kwanta Dama A Gobarar Tashar Jirgin Ruwan Shahid Raja’i Sun Kai 21
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno
  • Gwamnatin Kano Ta Gano  An Biya Wasu Ma’aikatan Bogi Naira Miliyoyi