Rahotanni da ke fitowa daga kasar suna nuni da cewa, Yawancin fararen hula da aka kashe a tashe-tashen hankulan da suka faru a wannan Juma’a, dakarun sabuwar gwamnatin kasar ta Syria ne suka kashe su, kamar yadda binciken kungiyar kare hakkin bil Adam ta (SOHR) ya tabbatar.

Ayyukan tashe-tashen hankulan sun yi sanadin Kisan mutuwar fararen hula 162 a lardunan gabar tekun Syria, ciki har da mata da kananan yara, in ji rahoton kungiyar ta SOHR.

Akasarin wadanda aka kashe dai kamar yadda aka gani a wasu fayafayin bidiyo da aka dauka, jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria ne da suke da alaka kungiyoyi masu tsatsauran ra’ayi irin su Tahrir Sham da makamantansu da suke da alaka da Alqaida ne suka kama mutanen, bisa tuhumar cewa suna da alaka da tsohuwar gwamnatin Bashar Assad, a kan haka suka yanke musu hukuncin kisa a nan take kuma suka kashe su.

Kungiyar ta ce wannan matakin na nuni da irin mawuyacin hali mai matukar hadari da Syria ta fada a ciki, inda ake ci gaba da cin zarafi  jama’a da kuma muzguna musu da sunan daukar fansa a kan tsiraru marasa rinjaye.

Wasu daga cikin Hotunan da aka dauka sun yadu a shafukan sada zumunta, wadanda suke nuni da manyan laifukan yaki. Rahoton ya ce wasu daga cikin faifan bidiyo sun nuna lokacin da jami’an tsaron sabuwar  suka harbe wasu ‘yan kasar Syria da ba su dauke da makami, wadanda aka wulakanta su kafin a yi musu kisan gilla.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yansanda A Najeriya Sun Kama Yan Kasar Pakistan Biyu Da Hakanni Wajen Sake Yan Kasashen Waje A Kasar

Yansanda a birnin Lagos na kudancin kasar sun kama wasu yan kasar Pakistan biyu wadanda suke da hannu dumu-dumi a cikin aikin kamawa don neman kudaden fansa daga hannun wani dan kasar ta Pakistan dan shekara 48 a duniya.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran sun nakalto daga kafafen yada labaran kasar wadanda suka ji kakakin yansan na jihar Lagos Chief Superintendent Benjamin Hundeyin yana cewa, yan kasar Pakisatn da suka kama a wani dauki da suka wanda aka sace don neman kudaden fansa sun kama a ranar 5 ga watan maris akwia Roman Gull dan shekara 19 da kuma Aftab Ahmed dan shekarera 28 a duniya kuma yan asalin kasar Pakistan ne, wadanda suka hada kansu da wasu gungun barayi don yin haka.

Ya ce barayin sun nemi dalar Amurka $34,000 ko naira miliyon 50 daga wajensa a matsayin kudaden fansa. Amma kamfanin da yake yiwa aiki sun bada naira miliyon guda kacal a cikin kwanaki uku, inda yan sanda suka shiga suka kuma kubutar da shi. Kuma yansanda suna kokarin gano sauran mutane 5 da suke rage cikin gungun yan fashin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 1,018 ne aka kashe a ci gaba da kisan kiyashi kan tsiraru a gabar tekun Syria
  • Iran : Wadanda Suka Dage Kan Tattaunawa Da Iran, Na Yi Ne Don Amfanin Kansu_ Jagora
  • Senegal, Ta Karbi Wasu Sansanonin Sojin Faransa A Kasar
  • Tashe-tashen Hankula Na Ci Gaba Da Yin Sanadin Rayuka A Siriya
  • Sin Za Ta Buga Karin Haraji Kan Wasu Hajojin Canada Da Ake Shigarwa Kasar Bayan Kammalar Bincike
  • Iran Da Iraki Sun Nuna Damuwa Kan Tashe-tahen Hankula A Siriya
  • An Kashe Mutum Akalla 70 A Yaki Tsakanin HKS Da Yan Tawaye A Kudancin Kasar Siriya
  • Yansanda A Najeriya Sun Kama Yan Kasar Pakistan Biyu Da Hakanni Wajen Sake Yan Kasashen Waje A Kasar
  • An Ayyana Dokar Ta-baci A Wasu Yankunan Siriya