Jigon APC Ya Fara Yunkurin Sulhunta Kwankwaso, Ganduje Da Shekarau
Published: 8th, March 2025 GMT
Ba Zaura kadai ba ne yake kokarin ganin a samu zaman lafiya a tsakanin ‘yan siyasar guda ukun. Sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC da suka hada da dan takarar mataimakin gwamnan jam’iyyar a zaben 2023, Murtala Sule Garo da kuma fitaccen dan siyasa, Baffa Babba Danagundi, sun yi irin wannan kira.
Kwankwaso, Ganduje, da Shekarau, wadanda dukkansu sun yi wa’adi biyu a matsayin gwamnan Kano, suna jam’iyyun siyasa daban-daban, kuma sun ci gaba da yin tasiri sosai a matakin kananan hukumomi, jiha, da kasa baki daya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ƙin yin sulhu da ’yan bindiga na haifar da alheri – Gwamnan Zamfara
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ce matsayarsa na ƙin amincewa a yi sulhu da ’yan bindiga na taimakawa wajen dawo da zaman lafiya a jihar.
Ya bayyana haka ne a ranar Alhamis yayin da yake karɓi baƙuncin Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Hassan Bala Abubakar.
An kama ’yan Pakistan biyu da laifin yin garkuwa a Legas HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Sheikh Hassan Jingir a JosAir Marshal Abubakar, ya ziyarci jihar domin yin ta’aziyya harin bam da rundunar sojin sama ta kai wa wasu mutane bisa kuskure.
Gwamna Lawal ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta canza matsayarta ba game da ƙin sasanci da miyagun mutane.
“Muna shaida wa kowa cewa ba za mu zauna da ’yan bindiga ba,” in ji shi.
“Hanyar da muka ɗauka tana haifar da sakamako mai kyau, kuma muna ganin zaman lafiya yana samuwa a Zamfara.”
Gwamnan ya kuma yaba da yadda jami’an tsaro ke hanzarin amsa kiran gaggawa a jihar.
“Ina gode wa Hafsan Sojin Sama saboda matakin gaggawa da ya ɗauka. Kafin wannan ziyarar, ya aike da manyan jami’ai domin jajanta mana.
“Wannan yana nuna ƙwazo da jajircewarsu wajen kare lafiyar mutanenmu,” in ji shi.
Hakazalika, Gwamna Lawal ya bayyana cewa ana gina sabon filin jirgin sama a Zamfara, kuma ya buƙaci a gina wajen ajiye jiragen rundunar sojin sama a ciki don ɗaukar matakan gaggawa kan matsalolin tsaro.
“Muna gina filin jirgin sama a Zamfara. Da zarar an kammala, muna fatan samun wajen ajiye jiragen sojin sama a cikinsa domin hanzarta ɗaukar matakan tsaro,” a cewarsa.
Air Marshal Hassan Abubakar ya gode wa gwamnan bisa yadda ya fahimci cewar harin da sojin rundunar suka kai ba da gangan ba ne.
Ya bayyana cewa sojojin sun kai hari ne bisa bayanan sirri kan ayyukan ’yan bindiga, amma daga baya aka gano cewa wasu ’yan sa-kai sun rasa rayukansu a dalilin harin.
Ya tabbatar wa mutanen Zamfara cewa rundunar sojin sama za ta ci gaba da inganta ayyukanta domin kauce wa irin wannan kuskure a nan gaba.