Ba Zaura kadai ba ne yake kokarin ganin a samu zaman lafiya a tsakanin ‘yan siyasar guda ukun. Sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC da suka hada da dan takarar mataimakin gwamnan jam’iyyar a zaben 2023, Murtala Sule Garo da kuma fitaccen dan siyasa, Baffa Babba Danagundi, sun yi irin wannan kira.

Kwankwaso, Ganduje, da Shekarau, wadanda dukkansu sun yi wa’adi biyu a matsayin gwamnan Kano, suna jam’iyyun siyasa daban-daban, kuma sun ci gaba da yin tasiri sosai a matakin kananan hukumomi, jiha, da kasa baki daya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kwankwaso Shekarau

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Kwara Za Ta Rufe Karbar Kudin Aikin Hajji A Ranar Juma’a

Hukumar Kula da Jin DDaɗin Alhazai ta Jihar Kwara ta ayyana ranar Juma’a 11 ga Afirilun 2025 a matsayin ranar ƙarshe da za a kammala biyan kuɗin aikin hajjin bana ga dukkan maniyyatan jihar.

Shugaban hukumar, Alhaji Abdulkadir Abdulsalam ne ya bayyana hakan a yayin wata hira da manema labarai a Ilori.

Alhaji Abdulkadir ya bayyana cewa jimillar kuɗin aikin hajjin bana ya kai naira miliyan 8,459,000.

Ya yi kira ga dukkan maniyyatan da suka  fara biyan kuɗi da su tabbatar sun kammala ragowar kuɗin kafin ranar ƙarshe, wato 11 ga Afrilu, domin ba za a ƙara lokaci ba.

Alhaji Abdulsalam ya kuma buƙaci maniyyatan da su gaggauta miƙa fasfo ɗin su na tafiya ƙasashen waje ga jami’ansu domin fara aikin biza ba tare da wani jinkiri ba, yana mai jaddada cewa fasfo mai inganci da ke da aƙalla watanni shida da fara amfani ne kawai za a amince da shi.

Ya bayyana cewa miƙa fasfo da wuri na da matuƙar muhimmanci domin kauce wa jinkiri ko rikice-rikicen da ka iya tasowa wajen fitar da biza a ƙarshe.

Alhaji Abdulsalam ya shawarci maniyyatan da su kasance masu ɗabi’a tagari da yayin zamansu a kasa mai tsarki.

Ya bayyana cewa kamfanin jirgin sama na Max Air ne aka bai wa alhakin jigilar  mahajjatan Jihar Kwara na shekarar 2025 hukumance, yana mai cewa hukumar alhazan na aiki kafada da kafada da kamfanin don tabbatar da tafiyar da aikin jigilar cikin kwanciyar hankali kuma akan lokaci.

 

Ali Muhammad Rabi’u 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Boko Haram na sake ƙwace ikon wasu yankuna a Borno — Zulum
  • Kyautar LEADERSHIP Ta Kara Zaburar Da Mu Kan Sauke Nauyin Al’ummar Jigawa Akanmu – Gwamna Namadi
  • Jihar Kwara Za Ta Rufe Karbar Kudin Aikin Hajji A Ranar Juma’a
  • Gwamnan Kano Ya Sadaukar Da Lambar Yabonsa Ga ‘Ya’yan Marasa Ƙarfi A Kano
  • Iran da Amurka zasu fara tattaunawa a Oman ranar Asabar
  • Sabon Tsarin Harajin Kwastam Na Amurka Ya Kwace ‘Yancin Sauran Kasashe
  • Jam’iyyar Labour Ta Yi Barazanar Dakatar Da Peter Obi Da Gwamna Otti
  • Fulham ta doke Liverpool bayan wasa 26 a jere ba tare da rashin nasara ba
  • Tsohon Gwamnan Oyo, Omololu Olunloyo, Ya Rasu Yana Da Shekaru 89
  • Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025