Jagoran kungiyar Ansar Allah ta kasar Yemen, Sayyed Abdul-Malik al-Houthi, ya baiwa masu shiga tsakani wa’adin kwanaki hudu na tabbatar da shigar da kayayyakin jin kai a Gaza, yana mai gargadin cewa idan har Isra’ila ta ci gaba da toshe hanyoyin kai kayan agaji a Gaza, to dakarun Yemen za su ci gaba da kai hare-hare kan jiragen ruwa masu alaka da Isra’ila.

A cikin wani jawabi da ya yi wanda aka watsa a gidajen talabijin na ciki da wajen kasar Yemen, Al-Houthi ya soki ta’annutin da  Isra’ila ke ci gaba da yi wa Falasdinu, yana mai jaddada cewa, rashin aiwatar da yarjejeniyar dakatar da bude wuta da kuma hana shigar da kayan agaji a Gaza da kuma ci gaba da killace yankin da Haramtacciyar Kasar Isra’ila ke yi, lamari ne mai matukar hadari.

Al-Houthi ya zargi Isra’ila da kin yin aiki da alkawuran da ta dauka a karkashin yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma a kan Gaza, musamman dangane da ayyukan jin kai, yana mai cewa Hamas ta cika dukkanin alkawullanta da kuma sauke nauyin da ya rataya a wuyanta, ta hanyar kiyaye wannan  yarjejeniyar.

Har ila yau Al-Houthi ya yi Allah wadai da zafafa hare-haren da Isra’ila ke kai wa a yankunan yammacin gabar kogin Jordan da kuma al-Quds, yana mai bayyana irin rawar da Isra’ila ke takawa wajen kara kai hare-hare kan Falasdinawa a matsayin laifin yaki.

Baya ga haka kuma, Ya soki yadda Amurka ke goyon bayan mamayar Isra’ila ido rufe a karkashin Shugaba Donald Trump, yana mai cewa goyon bayan Washington ya karfafa gwiwar Isra’ila wajen ci gaba da muzgunawa Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila ke

এছাড়াও পড়ুন:

Yemen Ta Maida Martani Kan Wasu Cibiyoyin Ajiyar Makamai A Yaffa Don Tallafawa Gaza

Sojojin kasar Yemen sun yi amfani da jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa kan cibiyoyin makamai na HKI wadanda suka Yaffa (tel aviv) saboda daukar fansa kan kashe-kashen da take yi a Gaza.

Tashar talabijin Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran YAF na kasar Yemen yana fadar haka a jiya Jumma’a, ya kara da cewa sojojin yahudawan sun kai hare-hare kan unguwar Shaja’iyya inda suka kashe Falasdinawa da dama.

Ya zuwa yanzu tun fara yakin tufanul Aksa, a cikin watan Octoban shekara ta 2023, falasdinawa kimani 51,000 sannan wasu 115,688 a gaza. Ta kuma rusa kimani kasha 90% na gine-ginen Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
  •  Tsoffin Ma’aikatan Hukumar Leken Asiri HKI  Mosad Sun Shiga Cikin Masu Kiran A Kawo Karshen Yaki Da Gaza
  • Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin
  • Jiragen Saman Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Luguden Wuta Kan Asibitin Baptist Da Ke Gaza
  • HKI Ta Jefa Boma-Bomai A Kan Asbiti Tilo Da Ya Rage Yake Aiki A Arewacin Gaza
  • Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • MDD: Mafi Yawancin Wadanda Yaki Ya Ci A Gaza Mata Ne Da Kananan Yara
  • Yemen Ta Maida Martani Kan Wasu Cibiyoyin Ajiyar Makamai A Yaffa Don Tallafawa Gaza