Tinubu ya bai wa Farfesa Jega muƙami a gwamnatinsa
Published: 8th, March 2025 GMT
Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa Tsohon Shugaban Hukumar INEC, Farfesa Attahiru Muhammadu Jega, a matsayin Mashawarci kuma Mai Kula da Shirin Gyaran Noma da Kiwo na Shugaban Ƙasa.
Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ne, ya tabbatar da naɗin cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a.
Shugaba Tinubu na fatan wannan naɗi zai kawo ci gaba a harkar noma da kiwo, tare da ƙarfafa yunƙurin raya ƙasa.
Farfesa Jega, wanda tsohon Shugaban Jami’ar Bayero ta Kano ne, ya kasance mataimakin shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Gyaran Noma da Kiwo tare da Shugaba Tinubu.
Kwamitin ya gabatar da shawarwari masu muhimmanci kan yadda za a inganta harkar noma da kiwo, ciki har da ƙirƙirar Ma’aikatar Kiwo, wacce yanzu haka ta ke da minista.
Jega mai shekara 68 a duniya, yana da ƙwarewa sosai a fannin shugabanci.
Yana cikin Kwamitin Shawara na Ƙasa da Ƙasa kan Zaɓe kuma shi ne Shugaban Majalisar Gudanarwa na Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kano.
Ya shugabanci INEC daga shekarar 2010 zuwa 2015, inda ya jagoranci ayyukan zaɓe a Najeriya a wannan lokaci.
A cikin sanarwarsa, Onanuga ya bayyana cewa naɗin Jega a matsayin mashawarci na musamman zai taimaka wajen ci gaba da aiwatar da shirin gyaran noma da kiwo da kuma tabbatar da nasarorin da aka riga aka samu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farfesa Jega Naɗi
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 4, Sun Sace 45 A Katsina
A ƙauyen Maikuma, da ke cikin ƙaramar hukumar Dandume ta Jihar Katsina, ana zargin wasu ƴan bindiga sun kashe mutane 4 sannan suka sace a ƙalla 45. Harin ya faru ne a daren Lahadi, lokacin da wata babbar tawagar ‘yan fashin ɗauke da makamai ta kai farmaki a cikin al’umma.
Shaidu sun bayyana cewa masu farmakin sun shige gidaje daga a jere a jere suna aiki har tsawon awanni kafin su gudu zuwa dajin da ke kusa da su tare da waɗanda suka sace.
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 10, Sun Ceto Mutane 101 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Da Zamfara. ‘Yan Bindiga Sun Kashe Kwamandan ‘Yan Sa-kai, Sun Jikkata Wasu A KatsinaDuk da ƙoƙarin jami’an tsaro, ba su samu nasarar bin ƴan bindigar ba zuwa bayan iyakar garin. Shugaban ƙaramar hukumar Dandume, Basiru Musa, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa adadin masu farmakin sun kai fiye da 100.
Musa ya nuna damuwa game da yadda hare-haren ke faruwa akai-akai, yana kira ga hukumomi su ƙara tsaurara matakan tsaro don kare al’ummomin da ke cikin hatsari. Hukumomin tsaro na Jihar Katsina har kawo yanzu ba su fitar da wata sanarwa ta hukuma ba game da lamarin ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp