Tinubu ya bai wa Farfesa Jega muƙami a gwamnatinsa
Published: 8th, March 2025 GMT
Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa Tsohon Shugaban Hukumar INEC, Farfesa Attahiru Muhammadu Jega, a matsayin Mashawarci kuma Mai Kula da Shirin Gyaran Noma da Kiwo na Shugaban Ƙasa.
Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ne, ya tabbatar da naɗin cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a.
Shugaba Tinubu na fatan wannan naɗi zai kawo ci gaba a harkar noma da kiwo, tare da ƙarfafa yunƙurin raya ƙasa.
Farfesa Jega, wanda tsohon Shugaban Jami’ar Bayero ta Kano ne, ya kasance mataimakin shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Gyaran Noma da Kiwo tare da Shugaba Tinubu.
Kwamitin ya gabatar da shawarwari masu muhimmanci kan yadda za a inganta harkar noma da kiwo, ciki har da ƙirƙirar Ma’aikatar Kiwo, wacce yanzu haka ta ke da minista.
Jega mai shekara 68 a duniya, yana da ƙwarewa sosai a fannin shugabanci.
Yana cikin Kwamitin Shawara na Ƙasa da Ƙasa kan Zaɓe kuma shi ne Shugaban Majalisar Gudanarwa na Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kano.
Ya shugabanci INEC daga shekarar 2010 zuwa 2015, inda ya jagoranci ayyukan zaɓe a Najeriya a wannan lokaci.
A cikin sanarwarsa, Onanuga ya bayyana cewa naɗin Jega a matsayin mashawarci na musamman zai taimaka wajen ci gaba da aiwatar da shirin gyaran noma da kiwo da kuma tabbatar da nasarorin da aka riga aka samu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farfesa Jega Naɗi
এছাড়াও পড়ুন:
An harbe shugaban ƙungiyar Miyetti Allah a Kwara
Wasu ’yan bindiga sun harbe shugaban ƙungiyar makiyaya Fulani ta Miyetti Allah reshen Jihar Kwara, Alhaji Idris Abubakar Sakaina.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 10 na daren ranar Asabar yayin da maharan suka biyo sawunsa suka harbe shi a ƙofar gidansa da ke yankin Oke Ose na birnin Ilorin.
Malaman Tsangaya Sun Bai wa Gwamna Inuwa Lambar Yabo Ta ‘Khadimul Qur’an’ Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — RahotoMuhammad Abdullahi, wani hadimin Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq kan hulɗa da al’umma da harkokin Fulani, ya tabbatar da faruwar lamarin.
“Eh, an kashe shi jiya da daddare. Wasu ’yan bindiga ne suka harbe shi.
“A yanzu haka ana shirin yi masa jana’iza, amma tun a jiya ’yan sanda sun zo sun fara bincike.”
Sai dai mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Kwara, Ejire Adeyemi Toun da wakilinmu ya tuntuɓa, ta buƙaci ya ba ta lokaci za ta waiwaye shi daga baya.
Bayanai sun ce marigayin mai shekaru 32 tsohon hadimi ne a wurin Shugaban Ƙaramar Hukumar Moro kuma ɗaya daga cikin shugabannin Matasa Fulani a Jihar Kwara.