Iran da Saudiyya sun jaddada wajabcin kara karfafa dangantakasu
Published: 8th, March 2025 GMT
Ministocin harkokin wajen Iran da Saudiyya sun tabbatar da aniyar kaasashensu na ci gaba da kara azama domin bunkasa alakoki a tsakaninsu a dukkanin bangarori.
Wannan dai na zuwa ne a yayin ganawar da ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Araghchi da takwaransa na kasar Saudiyya Faisal bin Farhan suka yi ne a wannan Juma’a a gefen taron gaggawa karo na 20 na ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar hadin kan kasashen musulmi a birnin Jeddah.
A yayin wannan ganawar, bangarorin biyu sun yi nazari kan matsayin dangantakar da ke tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kuma masarautar Saudiyya, tare da jaddada aniyar kasashen biyu na ci gaba da fadada hadin gwiwa tsakaninsu.
Bangarorin biyu sun kuma yi nazari kan halin da ake ciki a kan batutuwa daban-daban da suka shafi yankin, da ma sauran batutuwa na kasa da kasa, tare da jaddada wajibcin yin hadin gwiwa a tsakanin dukkanin kasashen musulmi wajen tinkarar kalubale dangane da batun Palastinu da Isra’ila ta mamaye, da kuma hana aiwatar da makarkashiyar da ake shiryawa da nufin share batun Palastinu, ta hanyar tilastawa al’ummar Gaza yin gudun hijira daga yankinsu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran : Samar Da Kasashe Biyu Baya Tabbatar Da ‘Yancin Falasdinawa
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya sake jaddada kin amincewa da matakin samar da kasashe biyu a matsayin samar da mafita ga rikicin falasdinu, yana mai cewa hakan ba zai tabbatar da hakkokin Falasdinawa ba, a maimakon haka ya ba da shawarar samar da “kasa dimokuradiyya guda daya” a matsayin mafita daya tilo.
Da yake jawabi yayin taron musamman na ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC, a birnin Jeddah na kasar Saudiyya da aka kira don magance cin zarafi da laifukan da Isra’ila ke yi kan al’ummar Falasdinu, Araghchi ya jaddada matsayar Iran kan Falastinu tare da bayyana goyon bayan da Tehran ke yi wa Falasdinawa a matsayin abin da ba za a iya mantawa da shi ba.
Araghchi ya kara da cewa, tare da mutunta ra’ayoyin wasu kasashe ‘yan’uwa kan batun samar da kasashe biyu, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta na kan ra’ayinta na cewa, wannan mafita ba za ta kai ga tabbatar da hakkin al’ummar Falastinu ba,” in ji Araghchi, yana mai jaddada matsayin Iran na bayar da shawarar kafa wata kasa ta dimokiradiyya wacce ke wakiltar dukkan ‘yan Falastinu.
Araghchi ya kuma yi kakkausar suka ga yunkurin gwamnatin Amurka na tilasta al’ummar Gaza kaura,” yana mai dagnata hakan da keta dokokin kasa da kasa, da yarjejeniyar Geneva ta hudu.”
Ya kuma bukaci kasashe mambobin kungiyar OIC da su aiwatar da irin wadannan matakai a matsayin wata hanya ta tursasawa gwamnatin sahyoniyawan ta dakatar da laifukan da take aikatawa kan al’ummar Gaza da sauran kasashen yankin.