Leadership News Hausa:
2025-03-09@12:20:14 GMT

Rikicin Shugabancin Majalisar Legas: Ko Sulhunsu Zai Dore?

Published: 8th, March 2025 GMT

Rikicin Shugabancin Majalisar Legas: Ko Sulhunsu Zai Dore?

Rikicin ya fara ne tun bayan tsige Obasa a ranar 13 ga Janairu, 2025, a matsayin shugaban majalisar. ‘Yan majalisa 33 a zaman da aka yi a wannan rana suka tsige Obasa tare da ayyana tsohowar mataimakiyar shugaban majalisar, Merand a matsayin shugaban majalisar dokokin Jihar Legas.

Ko da yake ’yan majalisar sun yi nuni da cewa yana cin zarafin mukami da karkatar da kudade da kuma rashin da’a a matsayin wani bangare na dalilan tsige Obasa, matakin ya nuna asalin rikicin da ya barke a majalisar ta 10 a jihar.

‘Yan majalisar dai sun tsige Obasa ne a lokacin da yake kasar Amurka.

Bayan dawowarsa Legas a ranar 25 ga Janairu, 2025, ya kalubalanci cire shi.

Duk da tsoma bakin manyan jiga-jigan jam’iyyar APC, musamman tsofaffin gwamnonin jihohin Osun da Ogun, Cif Bisi Akande da Cif Olusegun Osoba, ba a warware rikicin shugabancin ba.

Ita ma majalisar ba da shawara kan harkokin mulki a jihar ta kasa shawo kan rikicin, inda wasu mambobin ke ganin cewa Shugaban kasa Bola Tinubu ne kadai zai iya shiga tsakani yadda ya kamata.

Sai dai duk da shiga tsakani da kwamitin sasantawa da Akande ya jagoranta da Tinubu ya shirya domin warware matsalar, da alama rikicin ya kara kamari. Kwamitin dai ya gana da ‘yan kungiyar GAC da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a jihar da kuma ‘yan majalisar, duk da haka bai hakarsa ba ta cimma ruwa ba.

A ranar Alhamis da ta gabata ne Obasa, wanda bai halarci majalisar ba tun bayan tsige shi, ya koma harabar majalisar a wani mataki na ban mamaki.

Matakin dai ya sanya masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa da sauran al’umma cikin kaduwa, yayin da sabon al’amarin ya kara jefa majalisar cikin rudani.

Duk da shigarsa ofishin, ‘yan majalisa 35 ne suka ki amincewa da Obasa, yayin da ‘yan majalisa hudu suka yi zaman da shi a wannan rana.

A zama na karshe da Meranda ta yi a matsayin shugaban, ta dage zaman majalisar tare da da’awar cewa ta zama shugaban majalisar dokokin Jihar Legas.

Yayin da take bayyana matakinta na yin murabus, Meranda ta ce ta yi hakan ne domin ceto majalisar daga rigingimu da abin kunya da bai kamata ba, tana mai jaddada cewa ta dauki matakin ne don karrama manyan shugabannin siyasa.

Ta yi alkawarin ba za ta rabu da tafarkin mutunci, adalci, rikon amana da hidimar mahaifinta Marigayi Cif Akanni Lawal Taoreed ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki shugaban majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar wakilai na shirin ƙwace rajistar jam’iyyu daga hannun INEC

Majalisar Wakilai na shirin kafa wata sabuwar hukuma da za ta karɓi ikon yin rajistar jam’iyyun siyasa daga Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).

Wannan na zuwa ne bayan da majalisar ta gabatar da wani sabon ƙudiri kan batun.

Sojoji sun hallaka mai haɗa wa Boko Haram bam a Sambisa Dakatarwa: Har yanzu ni Sanata ce — Natasha

Kakakin Majalisar, Hon. Tajudeen Abbas, tare da Hon. Marcus Onobun daga Jihar Edo ne, suka gabatar da ƙudirin.

Ƙudirin na neman kafa wata hukuma mai zaman kanta da za ta riƙa yi wa jam’iyyu rajista, kula da dokokinsu, da kuma tallafa musu.

Har ila yau, ƙudirin na neman a kafa wata kotu ta musamman da za ta duba ƙorafe-ƙorafen da suka shafi jam’iyyu da rikice-rikicen da ke tasowa a tsakaninsu.

A cewar Hon. Marcus Onobun, wannan matakin ya zama dole domin kawo ƙarshen rikice-rikicen cikin gida da ke addabar jam’iyyun siyasa a Najeriya.

A halin yanzu, ƙudirin ya tsallake karatu na biyu a majalisar, lamarin da ke nuni da cewa ana iya ci gaba da duba yiwuwar aiwatar da shi a nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da muka dakatar da Sanata Natasha — Majalisar Dattawa
  • Gwamnati: Najeriya Ta Yi Asarar Tiriliyoyin Naira Kan Hakar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Zan sasanta Akpabio da Natasha — Ministar Harkokin Mata
  • Majalisar wakilai na shirin ƙwace rajistar jam’iyyu daga hannun INEC
  • Dakatarwa: Har yanzu ni Sanata ce — Natasha
  • Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Sanata Natasha Na tsawon Watanni 6 Saboda Rashin Da’a
  • Xi Jinping Ya Ziyarci Mambobin Majalisar CPPCC
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha na Watanni 6
  • Ƴar Majalisar Dattawa Natasha Akpoti Na Fuskantar Dakatarwar Wata Shida