“Bisa ga ajandar sabunta fata na Shugaba Tinubu, mun himmatu wajen tabbatar da manufofi da ka’idojin da suka jagoranci hukumar tsawon shekaru.

“Ina kuma tabbatar wa ‘yan Nijeriya, musamman maniyyatan da suka yi niyyar zuwa aikin hajjin 2025, za su gode wa Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da NAHCON bisa sakamakon aikin hajjin 2025.

“Shugaban kasa yana tsayawa kan Magana daya. Yana ba mu dukkan goyon bayan da ya kamata. Ba za mu ci amanarsa ba. Ba za mu sauka daga kan manufarmu ba.

“A kan wannan, dole ne mu gode wa Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima bisa yadda suka ba mu amanar tafiyar da harkokin aikin hajji.

“Hukumar ta samu wasu nasarorin da suka shahara a cikinsu akwai kwato sama da naira biliyan biyar na ayyukan da ba a yi wa maniyyata aikin hajjin 2023 ba, wanda ya nuna jajircewarmu na yin aiki da gaskiya da kuma kare muradun mahajjatan Nijeriya.

“Mun kuma yi aiki tare da Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya don tabbatar da bayar da fasfo na maniyyata a kan lokaci.

“A hankali a hankali muna aiwatar da wasu muhimman tsare-tsare don tabbatar da gudanar da aikin hajjin 2025 cikin kwanciyar hankali, musamman dangane da samar da ayyukan jin dadin maniyyatanmu.”

Sai dai Farfesa Abdullahi Sale ya yi kira ga masu ruwa da tsaki da su ci gaba da mara wa ayyukan hukumar baya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji biyu da gomman ’yan ta’adda sun rasu a artabu a Borno

Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne sun kai hari kauyen Izge da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza a Jihar Borno, inda suka kashe sojoji tare da rasa mayaƙansu da dama.

Rahotanni na cewa harin ya auke ne da misalin karfe 1:00 na ranar Lahadi a lokacin da ’yan ta’addan suka mamaye sansanin sojin Nijeriya da ke garin Izge.

Zanga-zangar da za mu yi babu gudu babu ja da baya — Take It Back An sayar da kare mafi tsada a duniya

Wata majiyar tsaro ta tabbatar wa Aminiya cewar wani soji mai muƙamin Kyaftin da kuma Kofur na daga cikin waɗanda suka kwanta dama, yayin da sojoji suka yi nasarar hallaka mahara da dama a yayin arangamar.

Shugaban ƙaramar Hukumar Gwoza, Hon. Abba Kawu Idrissa Timta, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Sai dai ya ce har yanzu lokacin da aka tuntuɓe shi ba a kai ga tantance irin asarar da rayuka daga ɓangarorin biyu ba.

“Sai dai muna tabbatar da kashe ’yan ta’adda da dama,” a cewarsa.

Bayanai sun ce mahara da dama haye a kan babura sun mamaye sansanin sojojin, bayan da suka harba makamin roka da ake kira RPG a kansu.

Rahotanni sun ce, da farko sun kama hanyar nasara a kan sojoji, sai daga bisani mafarauta da ’yan banga suka ƙara ƙwarin guiwa har ta kai ga fatattakar maharan.

Majiyoyi sun ce sojoji da mafarauta da jajirtattun mazauna garin ne suka fatattaki ’yan ta’addan da ke tserewa zuwa dajin Sambisa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Li Qiang Ya Tattauna Da Shugabar Kwamitin EU
  • Pezeshkian: Dole ne Amurka ta tabbatar da cewa da gaske take yi a game da tattaunawa
  • HOTUNA: Yadda zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu ta gudana a wasu biranen Nijeriya
  • Saudiyya ta musanta hana ’yan Nijeriya biza
  • HOTUNA: Zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu ta ɓarke a Abuja da Legas
  • Sojoji biyu da gomman ’yan ta’adda sun rasu a artabu a Borno
  • Ya Kamata A Yi Adawa Da Kama Karya A Tabbatar Da Adalci
  • Nazarin CGTN: An Bukaci Kasa Da Kasa Su Bijirewa Cin Zali Daga Amurka
  • Wani Kwararre Ya Bukaci A Rungumi Fahasar Zamani Don Bunkasa Aikin Noma A Nijeriya
  • Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025