Aminiya:
2025-04-09@11:45:54 GMT

Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a Kano

Published: 8th, March 2025 GMT

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, ta rufe wani shagon da ake yin caca na zamani, wanda aka fi sani da “betting.

Mataimakin kwamandan hukumar a Kano, Sheikh Mujahideen Aminudeen, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudanar a Kano.

Kotu ta yanke wa dillalan ƙwayoyi hukuncin ɗaurin shekaru 95  Kisan malami: Shugabannin Kiristocin Kudancin Kaduna sun yi Allah-wadai

Ya ce sun ɗauki wannan mataki ne bisa dokokin Jihar Kano, kuma hukumar ta kai samame wajen kafin ta rufe shagon gaba ɗaya.

Aminudeen ya nuna damuwa kan yadda wasu Musulmai ke shiga harkar caca, musamman a lokacin azumin watan Ramadan.

A watannin baya hukumar ta haramta yin cacar “betting” lamarin da ya sanya ta fara farautar wuraren da ake yin cacar domin rufe su.

An fara aiki da dokokin shari’ar Musulunci a Kano tun shekarar 2000, kamar yadda ake yi a wasu jihohi 11 na Arewacin Najeriya.

Waɗannan dokoki sun haramta caca, karuwanci da shan giya a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ramadan Shari ar Musulunci

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Kano Ya Sadaukar Da Lambar Yabonsa Ga ‘Ya’yan Marasa Ƙarfi A Kano

LEADERSHIP tana karrama mutane da ƙungiyoyin da suka taka rawar gani a fannoni daban-daban kamar gwamnati, kasuwanci da al’umma.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu Ta Daure Ango Kan Liƙi Da Kuɗi A Wajen Bikinsa A Kano
  • Sanusi II Ya Naɗa Sabon Galadiman Kano
  • Jihar Kwara Za Ta Rufe Karbar Kudin Aikin Hajji A Ranar Juma’a
  • Kotu ta daure ango wata 6 saboda likin kudi a bikinsa
  • Gwamnan Kano Ya Sadaukar Da Lambar Yabonsa Ga ‘Ya’yan Marasa Ƙarfi A Kano
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Ci Gaba Da Gudanar Da Taron Bita Ga Alhazai
  • Mahara sun yi garkuwa da fiye da mutum 50 a Katsina
  • Dangantaka ta yi tsami tsakanin Aljeriya da kasashen kawancen Sahel
  • Ƴansanda Sun Janye Gayyatar Sarki Sunusi, Zasu Zo Kano Da Kansu
  • Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya