HausaTv:
2025-04-09@06:28:23 GMT

Iran Da Iraki Sun Nuna Damuwa Kan Tashe-tahen Hankula A Siriya

Published: 8th, March 2025 GMT

Kasashen Iran da kuma Iraki sun nuna damuwa kan tashe tashen hankulan dake faruwa a Siriya.

A wata sanarwa da ta fita ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta bayyana matukar damuwarta kan yadda tashe-tashen hankulan da ke yaduwa a fadin kasar ta Siriya, tana mai gargadin cewa, wannan yanayi mara kyau zai share fagen rashin zaman lafiya a yankin da kuma kara tunzura Isra’ila.

Kakakin ma’aikatar Esmail Baghai ya bayyana cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran na nuna damuwa kan rashin tsaro, tashe-tashen hankula, zubar da jini da cutar da al’ummar Siriya da basu ji basu gani ba.

Ita ma ma’aikatar harkokin wajen kasar Iraki ta bayyana matukar damuwarta kan halin da ake ciki a makwabciyarta Syria, tana mai jaddada cewa karuwar tashe-tashen hankula a kasar Larabawar ka iya yin tasiri sosai ga tsaro da zaman lafiyar yankin.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a Asabar din nan, ma’aikatar ta jaddada bukatar “kare fararen hula daga bala’in rikici.”tare da yin kira da a ba da fifiko wajen tattauna hanyoyin warware matsalar ta cikin lumana.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da wasu majiyoyi na cikin gida suka bayar da rahoton cewa, an gwabza kazamin fada tsakanin bangarorin da ke da alaka da gwamnatin Hayat Tahrir al-Sham (HTC) mai mulki da kuma ‘yan adawa masu biyayya ga tsohuwar gwamnatin, kusa da asibitin al-Watani da ke birnin As-Suwayda a kudu maso yammacin kasar Syria.

Kungiyar kare hakkin dan adam ta Syrian Observatory for Human Rights (SOHR) mai hedkwata a birnin Landan ta bayar da rahoto a jiya Juma’a cewa akalla mutane 237 ne aka kashe a yankin gabar tekun Syria tun bayan barkewar sabon tashin hankali a ranar Alhamis.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya ta musanta hana ’yan Nijeriya biza

Ƙasar Saudiyya ta musanta batun da ake yaɗawa cewa  ta sanya Najeriya a jerin ƙasashen da ta hana biza.

Sanarwar da aka yaɗa a kafofin sadarwa ta bayyana cewa daga ranar 13 ga Afrilu, Saudiyan za ta daina bai wa ƙasashen Masar, India, Pakistan, Morocco, Tunisa, Yemen da Aljeria bizar aiki, ta ziyara, da ta yawon buɗe idanu.

Lakurawa sun kashe ’yan sa-kai 13 a Kebbi HOTUNA: Zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu ta ɓarke a Abuja da Legas

“Rashin yin biyayya ga wannan tsarin ka iya jawo haramta shiga kasar sawon shekaru biyar” a cewar sanarwar.

Sai dai Cibiyar yawon buɗe ido ta Saudiyya ta bayyana wa manema labarai cewa waɗannan sabbin dokokin sun takaita ne ga lokacin aikin hajji.

“Duk wanda ke da bizar ziyara, ba zai yi aikin Hajji ko zama a birnin Makka ba tun daga ranar 10 har zuwa 14 ga Thul Qida. Bizar aikin Hajji za ta yi aiki ne kawai daga lokacin Hajjin.”

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Tattaunawa kai tsaye da Amurka a yanzu ba shi ne zabinmu ba
  • Faransa, Masar da Jordan sun yi kira da a tsagaita wuta cikin gaggawa a Gaza
  • Tsofaffin Ma’aikatan FRCN Za Su Gudanar da Zanga-zanga Kan Jinkirin Biyan Hakkokin Su
  • Arakci: Amruka Tana Mafarkin Kulla Yarjejeniya Da Iran Kwatankwanci Wacce Ta Yi Da Kasar Libya
  • Saudiyya ta musanta hana ’yan Nijeriya biza
  • ACF Ta Bukaci Gwamnatin Najeriya Da Ta Kawo Karshe Tashe-Tashen Hankula Filato
  • Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya
  • Trump Ya Yada Hutunan Bidiyo Wadanda Suka Nuna Yadda Sojojin Amurka Suka Kashe Mutanen Yemen Wadanda Suke Bukukuwan Salla Karama
  • Burtaniya Ta Soki Gwamnatin Netanyahu Kan Hana ‘Yan Majalisarta Biyu Shiga Cikin Isra’ila
  • Finafinan Kannywood da suke tashe da kuma manyan marubutansu