HausaTv:
2025-04-29@10:52:41 GMT

Iran Da Iraki Sun Nuna Damuwa Kan Tashe-tahen Hankula A Siriya

Published: 8th, March 2025 GMT

Kasashen Iran da kuma Iraki sun nuna damuwa kan tashe tashen hankulan dake faruwa a Siriya.

A wata sanarwa da ta fita ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta bayyana matukar damuwarta kan yadda tashe-tashen hankulan da ke yaduwa a fadin kasar ta Siriya, tana mai gargadin cewa, wannan yanayi mara kyau zai share fagen rashin zaman lafiya a yankin da kuma kara tunzura Isra’ila.

Kakakin ma’aikatar Esmail Baghai ya bayyana cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran na nuna damuwa kan rashin tsaro, tashe-tashen hankula, zubar da jini da cutar da al’ummar Siriya da basu ji basu gani ba.

Ita ma ma’aikatar harkokin wajen kasar Iraki ta bayyana matukar damuwarta kan halin da ake ciki a makwabciyarta Syria, tana mai jaddada cewa karuwar tashe-tashen hankula a kasar Larabawar ka iya yin tasiri sosai ga tsaro da zaman lafiyar yankin.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a Asabar din nan, ma’aikatar ta jaddada bukatar “kare fararen hula daga bala’in rikici.”tare da yin kira da a ba da fifiko wajen tattauna hanyoyin warware matsalar ta cikin lumana.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da wasu majiyoyi na cikin gida suka bayar da rahoton cewa, an gwabza kazamin fada tsakanin bangarorin da ke da alaka da gwamnatin Hayat Tahrir al-Sham (HTC) mai mulki da kuma ‘yan adawa masu biyayya ga tsohuwar gwamnatin, kusa da asibitin al-Watani da ke birnin As-Suwayda a kudu maso yammacin kasar Syria.

Kungiyar kare hakkin dan adam ta Syrian Observatory for Human Rights (SOHR) mai hedkwata a birnin Landan ta bayar da rahoto a jiya Juma’a cewa akalla mutane 237 ne aka kashe a yankin gabar tekun Syria tun bayan barkewar sabon tashin hankali a ranar Alhamis.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya  Suke Bukata

Shugaban kasar Siriya ya ki amincewa da bukatar kurdawan kasar daga dakarun Democradiyyan  kurdawa wato (SDF), na samar da tsarin tarayya a kasar bayan kifar da gwanatin Basshar Al-Asab.

Jaridar The Nation ta nakalto shuga Al-Ahmad Sharaa yana fadar haka a jiya Lahadi ya kuma kara da cewa tsarin tarayyar barazana ce ga hadin kan kasar ta Siriya sannan tsarin tarayya ya sabawa yarjeniyar da aka kulla da kurdawan a baya-bayan nan.

A wani taron da suka gabatar a makon da ya gabata,  jam’iyyar kurdawan kasar ta Siriya (SDC) ta fadawa “ The National  ”  bayan taron kan cewa suna bukatar tsarin tarayyar a kasar Siriya don shi ne kadai zai tabbatar da hakkinsu a kasar.

A cikin watan maris da ya gabata ne shugaba Al-Sharaa na kasar Syriya ya rattaba hannu a kan wata yarjeniya da shugaban dakarun kurdawan kasar Siriya SDF Mazlum Abdi dangane da hade dakarunsa da sojojin kasar Siriya, sannan yace tsarin tarayya ya sabawa wannan yarjeniyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al-Shara Ya Ki Abincikewa Da Tsarin Tarayya Wanda Kurdawan Kasar Siriya  Suke Bukata
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Fira Ministan Indiya Ya Bayyana Cewa: Iran Tana Kokari A Fagen Inganta Zaman Lafiya A Yanki Da Duniya Baki Daya
  • Amurka Ta Ce: Shugaban Rikon Kwarayar Siriya Al-Julani Ya Yi Alkawarin Cewa Ba Zai Cutar Da Tsaron Isra’ila Ba
  • Hamas Ta Yi Allawadai Da Dage Rigar Kariya Na Ma’aikatar Hukumar UNRWA
  • Iran ta Bayyana cewa: TattaunawarMuscat Wata Dama Ce Ta Samun Zaman Lafiya Kan Batutuwan Masu Sarkakiya
  • Wang Yi Ya Ce Kasar Sin Za Ta Magance Cin Zarafin Da Amurka Ke Yi Ita Kadai
  • Zulum Ya Nuna Damuwa Kan Yadda Boko Haram Ke Dawowa Wasu Yankuna A Borno
  • Gwamnatin Siriya Zata Samar Da Huldar Jakadanci Da HKI A Dai-Dai Lokacinda Ya Dace
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Siriya Ya Bukaci MDD Ta Dagewa Kasarsa Takunkuman Tattalin Arziki