HausaTv:
2025-03-09@12:04:15 GMT

Bankin Duniya : Sake Gina Lebanon Yana Bukatar Dala Biliyan 11

Published: 8th, March 2025 GMT

Bakin duniya ya kiyasta cewa ana bukatar dala biliyan 11, domin sake gina Lebanon sakamakon barnar da hare haren Isra’ila suka haifarwa kasar.

Bangaren gidaje na Lebanon ya fi fama da matsalar, inda aka kiyasta asarar da ta kai dala biliyan 4.6, yayin da masana’antar yawon bude ido ta yi asarar dala biliyan 3.

6.

“Sakamakon rikice-rikicen ya haifar da raguwa a ainihin GDP na Lebanon na 7.1 bisa dari a 2024,” in ji Bankin Duniya.

Rahoton ya kara da cewa, “Ya zuwa karshen shekarar 2024, raguwar GDP na kasar Lebanon tun daga shekarar 2019 ya kusan kashi 40%, wanda hakan ya haifar da koma bayan tattalin arziki a bangarori da dama da kuma yin tasiri ga ci gaban tattalin arzikin kasar.”

Sojojin Isra’ila sun fara kai farmaki kan sansanonin Hizbullah a kudancin Lebanon jim kadan bayan kaddamar da kisan kiyashi a zirin Gaza da aka yiwa kawanya a watan Oktoban shekarar 2023.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Yahudawa 800 Sun Kutsa Cikin Kasar Lebanon A Yau Juma’a

Kafafen watsa labarun HKI sun ambaci cewa a yau Juma’a yahudawa 800 sun kutsa cikin iyakar Lebanon, zuwa kabarin wani malamin yahudawa Rabbi Ashi. Sun kuwa isa wurin ne a karkashin rakiyar sojojin mamaya.

Majiyar ‘yan sahayoniyar ta ce, kabarin malamin yahudawan dai yana a cikin iyakar Lebanon ne dake kallon matsugunin ‘yan share wuri zauna ta Mir Gliot.

A cikin makwanni kadan da su ka gabata dai yahudawan ‘yan share wuri zauna sun rika ketaro iyaka daga Falasdinu dake karkashin mamaya zuwa Lebanon, sai dai na yau Juma’a ne mafi girman adadin yahudawan da suka ketara iyaka.

Ya zuwa yanzu dai babu wata sanarwa da ta fito daga sojojin Lebanon ko gwamnati akan abinda ya faru. Amma a jiya Alhamis dai rundunar sojan kasar ta Lebanon ta fitar da sanarwa da a ciki ta bayyana cewa; Duk da cewa a akwai tsagaita wutar yaki amma Isra’ila tana ci gaba da keta hurumin kasar Lebanon ta kasa, ruwa da kuma sama.” Sanarwar ta kuma ce; Abinda Isra’ilan take yi,barazana ce ga zaman lafiya a cikin Lebanon da kuma wannan yankin.

Haka nan kuma rundunar sojan kasar ta Lebanon ta bayyana cewa; Sojojin na mamaya suna ci gaba da kai wa mutane hare-hare a garuruwan kudancin Lebanon da kuma  yankin Bik’a.

A cikin wannan halin, mutanen kudancin kasar ta Lebanon suna ci gaba da komawa garuruwansu duk da cewa suna fuskantar hastarin kai musu daga sojojin mamaya.

Tun a ranar 26 ga watan Nuwamba ne dai aka tsagaita wutar yaki a tsakanin Lebanon da HKI bisa cewa za ta janye daga wuraren da ta yi kutse a cikin kwanaki 60, sai dai kuma hakan ba ta faru ba. Kungiyar Hizbullah ta sha yin kira ga gwamnati da ta yi amfani da hanyoyin diplomasiyya domin tilastawa ‘yan mamayar janyewa, kafin a shiga wata magana ta daban.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugabannin Larabawa Sun Amince Da Tsarin Gina Gaza Da Zai Lakume Dala Biliyan 53
  • Kasashen Turai sun goyi bayan shirin Larabawa na sake gina Gaza
  • Qatar Ta Ce Bata Goyon Bayan Yakin Don Warware Shirin Nukliyar Kasar Iran
  • Aikin Noma Ya Ragu Da Kashi 1.8 A Zango Na Hudu A Shekarar 2024
  • Zuwa Karshen Fabarairu Yawan Musayar Kudaden Da Aka Adana Na Sin Ya Kai Dala Tiriliyan 3.2272
  •  Yahudawa 800 Sun Kutsa Cikin Kasar Lebanon A Yau Juma’a
  • Asusun Ajiyar Nijeriya Na Ketare Ya Ragu Da Dala Biliyan Biyu A 2025
  • An Yi Hada- hadar Dala 1 Kan Naira 1,500 A Kasuwannin Musayar Kudi
  • Yadda Fadada Bude Kofar Kasar Sin Ke Haifar Da Damammaki Ga Duniya