Sojojin Isra’ila sun kai farmaki kan wasu masallatai a birnin Nablus da ke gabar yammacin kogin Jordan a ranar Juma’a ta farko ta watan Ramadan.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto cewa, a safiyar ranar Juma’a sojojin gwamnatin Isra’ila sun kutsa kai cikin wasu masallatai shida na birnin Nablus, inda suka hana gudanar da salla.

Har ila yau, sun kame wasu Falasdinawa uku a lokacin da suke kutsawa cikin Nablus.

Rahotanni sun ce sojojin na Isra’ila sun harba harsasai masu rai, da gurneti da bama-bamai masu guba a yayin da dakarunsu suka mamaye wasu unguwanni a birnin.

Ko a ranar Alhamis din da ta gabata hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa ci gaba da cin zarafi da gwamnatin Isra’ila ke yi kan yankin yammacin kogin Jordan na daga cikin shirin gwamnatin kasar na mamaye yankin.

A watan Yulin 2024, Kotun Duniya (ICJ) ta yanke hukuncin mamayar da Isra’ila ta dade tana yi a yankunan Falasdinawa ba bisa ka’ida ba, inda ta bukaci a kwashe duk wasu haramtattun matsugunan da ke Yammacin Kogin Jordan da gabashin Quds.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila sun

এছাড়াও পড়ুন:

Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a Kano

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, ta rufe wani shagon da ake yin caca na zamani, wanda aka fi sani da “betting.

Mataimakin kwamandan hukumar a Kano, Sheikh Mujahideen Aminudeen, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudanar a Kano.

Kotu ta yanke wa dillalan ƙwayoyi hukuncin ɗaurin shekaru 95  Kisan malami: Shugabannin Kiristocin Kudancin Kaduna sun yi Allah-wadai

Ya ce sun ɗauki wannan mataki ne bisa dokokin Jihar Kano, kuma hukumar ta kai samame wajen kafin ta rufe shagon gaba ɗaya.

Aminudeen ya nuna damuwa kan yadda wasu Musulmai ke shiga harkar caca, musamman a lokacin azumin watan Ramadan.

A watannin baya hukumar ta haramta yin cacar “betting” lamarin da ya sanya ta fara farautar wuraren da ake yin cacar domin rufe su.

An fara aiki da dokokin shari’ar Musulunci a Kano tun shekarar 2000, kamar yadda ake yi a wasu jihohi 11 na Arewacin Najeriya.

Waɗannan dokoki sun haramta caca, karuwanci da shan giya a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Sahayoniya ta hana Falasdinawa masu ibada yin I’itikafi a Masallacin Al-Aqsa
  • Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan
  • A ranar Mata Ta Duniya, Hamas Ta Yi Allawadai Da Kashe Mata 12,000 A Gaza
  • Dalilin da muka dakatar da Sanata Natasha — Majalisar Dattawa
  • Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a Kano
  • GORON JUMA’A
  • MDD Ta Nuna Damuwarta Da Abinda ke Faruwa A Yankin Yamma Da Kogin Jordan
  • Araghchi Ya Tafi Saudiyya Domin Halartar Taron OIC
  • Hukumar Zaɓen Neja ta sanar da ranar zaɓen ƙananan hukumomoni