Shugaba Bola Tinubu ya nada tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, Farfesa Attahiru Muhammadu Jega a matsayin mai ba da shawara na musamman kan sake fasalin kiwon dabbobi.

Shugaban ya yi fatan nadin Farfesa Jega zai haifar da ci gaba mai ma’ana a fannin kiwo, da kuma kara karfafa ayyukan ci gaban kasa.

Tsohon Mataimakin Shugaban Jami’ar Bayero ta Kano, Farfesa Jega ne ya jagoranci Kwamitin Kiwo na Shugaban Kasa tare da Shugaba Tinubu.

Wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan yada labarai Bayo Onanuga ya fitar, ta ce kwamitin ya bayar da cikakkun shawarwarin da suka tabbatar da sauye-sauyen da aka samu a fannin kiwon dabbobi, daya daga cikinsu shi ne samar da ma’aikatar kiwo.

Jega, mai shekaru 68, mamba ne a Majalisar Ba da Shawarar Zabe ta Duniya, kuma Shugaban Majalisar Gudanarwa na Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Jihar Kano.

Ya rike mukamin shugaban hukumar ta INEC tsakanin shekarar 2010 zuwa 2015.

Sanarwar ta ce nadin nasa zai karfafa nasarorin da kwamitin shugaban kasa ya samu, tare da tabbatar da ci gaba da sauye-sauyen da aka fara gudanarwa.

Daga Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kisan Isuhu Yellow: ’Yan bindiga sun kai harin ɗaukar fansa

Wasu ’yan bindiga a ranar Lahadin da ta gabata sun kai harin ɗaukar fansar kashe ƙasurgumin ɗan ta’addan nan, Kachalla Isuhu Yellow da aka fi sani da Ɗan Isuhu.

’Yan ta’addan sun kai harin ne ƙauyen Keta da ke Ƙaramar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara, domin ɗaukar fansar kashe jagoransu da jami’an tsaro suka yi makonni biyu da suka gabata.

Kotu ta daure ango wata 6 saboda likin kudi a bikinsa Gaza: Isra’ila ta kashe Falasdinawa 58 a awa 58

Mazauna sun ce maharan sun kashe mutum ɗaya yayin da suka ƙone motoci 11 sannan kuma suka wawushe kayayyaki a kantinan ’yan kasuwa a yayin harin.

Bayanai sun ce ana zargin ’yan ta’addan da suka kai wannan hari mayaƙan Adamu Aliero ne — yayan marigayi Ɗan Isuhu.

Kachalla Yellow wanda ake alaƙantawa da kai munanan hare-hare a Zamfara da kuma babbar hanyar Funtua zuwa Gusau, ya gamu da ƙarshensa ne a yayin wani artabu da wata rundunar haɗin gwiwa ta Asakarawan Zamfara da kuma jami’an ’yan sanda a ƙauyen Keta.

A yayin da wasu rahotanni ke cewa, Ɗan Isuhu ya yi gamo da ƙarshensa ne a hannun wasu ’yan ta’adda masu adawa da shi da ke yi wa Dogo Gide mubaya’a, wasu kuma na cewa dakarun soji ne suka kawar da shi daga doron ƙasa.

Wani mazauni Danjigba — wani yanki da ke makwabtaka da Keta — ya tabbatar da cewa an kashe Isuhu Yellow ne a yayin da yake yunƙurin yi wa jami’an tsaro kwanton ɓauna a hanyarsu ta zuwa ƙauyen Keta domin kai ɗauki.

“Shi da mayaƙansa sun yi ƙoƙarin yi wa jami’an tsaron kwanton ɓauna amma a yayin musayar wuta da su aka kashe shi tare da mayaƙansa da dama.”

Ya ƙara da cewa, ragowar ’yan ta’adda a hanyarsu ta tserewa sun kai wa mazauna Danjigba hari, inda suka kashe mutum takwas ciki har da wani ɗan uwansa da wawushe kuɗi a hannun ’yan kasuwa.

Duk da aukuwar wannan hari, sai dai mazauna suka yi murnar mutuwar Isuhu Yellow, suna masu bayyana shi a matsayin marar imani wanda ya ɗauki alhakin sacewa da zubar da jinin mutane da dama a Tsafe, Gusau, Dan Sadau da kuma Funtua.

Kakakin rundunar ’yan sandan Zamfara, DSP Yazid Abubakar, ya tabbatar da kashe Isuhu Yellow a wani aikin haɗin gwiwa na jami’an tsaro da suka daƙile harin da aka kai ƙauyen Keta.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta karbi Amurkawa 3 da suka yi yukurin juyin mulki a Congo
  • Kisan Isuhu Yellow: ’Yan bindiga sun kai harin ɗaukar fansa
  • Yan Sanda A Saudiya Sun Tsare Wata Bafalasdinya Saboda Bayyana Tutar Kasarta A Kan Jakarta A Masallacin Ka’aba
  • Pezeshkian: Dole ne Amurka ta tabbatar da cewa da gaske take yi a game da tattaunawa
  • HOTUNA: Yadda zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu ta gudana a wasu biranen Nijeriya
  •  Kasashen Iran, Rasha Da China Za Su Yi Taro A Moscow Domin Tattauna Batutuwa Da Dama
  • HOTUNA: Zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu ta ɓarke a Abuja da Legas
  • Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Kananan Cibiyoyin Kiwon Lafiya 8,880 A Duka Fadin Kasar
  • Araqchi: Iran ba ta da matsala game da tattaunawa amma ba za ta lamunci yi mata barazana ba