Aminiya:
2025-04-09@00:29:14 GMT

Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol

Published: 8th, March 2025 GMT

Wata kotu a Koriya ta Kudu, ta saki tsohon shugaban ƙasar, Yoon Suk Yeol, bayan da ta yi watsi da kama shi, duk da cewa ana ci gaba da bincike kan zargin da ake masa.

Yoon, wanda aka dakatar daga mulki, an tsare shi ne tun a watan Janairu bayan da ake zarginsa da ƙoƙarin kifar da mulkin farar hula.

Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a Kano An kashe shugaban Lakurawa, Maigemu a Kebbi

A ranar 3 ga watan Disamban 2024, jami’an tsaro sun kai masa samame bisa zargin tayar da zaune tsaye.

Bayan an sake shi, Yoon ya fito daga gidan yari yana murmushi, sannan ya sunkuyar da kai domin nuna godiya ga magoya bayansa da suka zo ganinsa.

A ranar Juma’a, kotu ta soke umarnin da aka bayar na kama shi, inda ta ce babu isassun hujjoji da ke tabbatar da laifin da ake zarginsa da shi.

Duk da haka, ana ci gaba da shari’a kan batun tsige shi daga mulki.

Masu gabatar da ƙara sun ce za su mayar da hankali kan gabatar da hujjoji a gaban kotu maimakon ɗaukaka ƙara kan sakinsa.

Idan har kotun tsarin mulki ta tabbatar da tsige shi, Koriya ta Kudu dole ne ta gudanar da sabon zaɓen shugaban ƙasa cikin kwanaki 60.

Duk da haka, ana sa ran za a ci gaba da shari’ar Yoon, ko da kuwa an sauke shi daga mulki gaba ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Koriya ta Kudu zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Gwamnan Oyo, Omololu Olunloyo, Ya Rasu Yana Da Shekaru 89

Olunloyo ya jagoranci jihar Oyo tsakanin 1 ga Oktoba, 1983 zuwa 31 ga Disambar 1983.

 

Rasuwar marigayi dan siyasar na kunshe ne a cikin wata sanarwa da tsohon Editan jaridar Nigerian Tribune, Barista Oladapo Ogunwusi ya fitar a ranar Lahadi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Jin-ƙai ce kan gaba wajen wawure kuɗin gwamnati — Tsohon Minista
  • ɗin aikatar Jin-ƙai ce kan gaba wajen wawure kudin gwamnati — Tsohon Minista
  • Kotu ta daure ango wata 6 saboda likin kudi a bikinsa
  • Kisan Janar Alƙali: Kotu ta ɗage shari’a zuwa 28 ga Mayu
  • Tsofaffin Ma’aikatan FRCN Za Su Gudanar da Zanga-zanga Kan Jinkirin Biyan Hakkokin Su
  • Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya
  • Tsohon Gwamnan Oyo, Omololu Olunloyo, Ya Rasu Yana Da Shekaru 89
  • Ana Ci Gaba Da Kai Ruwa Rana Takanin Amurka Da China Kan Batun Harajin Fito
  • Guteress : ba wadan zai ci ribar yakin cinikayya
  • Amurka ta soke duk wata takardar izinin shiga kasar da aka baiwa ‘yan Sudan ta Kudu