Leadership News Hausa:
2025-04-09@00:19:55 GMT

Halayen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (2)

Published: 8th, March 2025 GMT

Halayen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (2)

3.Mai dauriya / hakuri

Hakuri yana da matukar kyau ace kana da shi a matsayinka na Malami ka kuma nunawa dalibai domin su ta shi da shi, wadanda kamar yadda aka yi bayani cikin maganar dabarun koyarwa,suna iya daukarka, a matsayin wanda za su rika yin koyi da kai saboda su koyi halinka na hakuri.Matukar akwai hakuri za a samu saukin yin aiki tare da kowadanne matsaloli ko fadi tashin da dalibi yake yi,wanda hakan na iya zama masa babban wani tarnaki wanda zai wuyar gano bakin zaren,ko kuma abin ya zama tamkar tafiyar Kura.

4. A rika yin abubuwan jawo ankali

Dalibai suna fara koyo ne tun lokacin da suke ‘yan yara hakan kuma ne ya basu damar fadawa Malamai cewar su gaji da yadda kai Malami/ko Malamai suke koya ma su.Matukar kana son ka yi dalilin yadda ajin na ka zai zama abin burgewa,don haka idan ka gano yadda lamarin yake,sai ka yi amfani da damar wajen kawo masu misalan ra’ayoyin da za su jawo hankalinsu,har abin ya shiga zuciyarsu da kuma maida hankalinsu kan abinda ake koya masu!

5.Rika saurare sosai

Yin saurare hakan na da amfani saboda gane matsalar da bada taimakon yadda za ayi maganin abin wato su matsaolin.Ka nemi a baka irin halin da ake ciki,bada kwarin gwiwa bil hakki da gaskiya, samar da hanyoyin da dalibai za su rika tuntubar ka a saukake,ka kuma tsaida hankalinka duk lokacin da kake saurare,ko wane lokaci ka yi kokarin gane manufa lokacin da ake yin magana,ka kuma lura dakyau yadda labarin zuciya yake lokacin d a kake magana ko ake yi maka.Yi kokarin sanin me yasa d a kuma dalilin da yasa za kayi hakan

6.Mai/ Masu son abinda suke koyawa

Masana ilimi ba wai kawai suna sha’awar aikin koyarwar bane bugu da kari ma suna da sha’awa ta daukar lokaci mai tsawo suna kasancewar su ta masu koyo,wanda irin haka yana nunawa a gwagwarmayar su ta masu koyarwa. Ci gaba da koyo da bunkasar kwarewar kwararru irin hakan yana matukar taimakawa ta yadda kwararru za su kasance koda yaushe suna cikin “shirin kota kwana”da kuma tunatar da Malamai da irin matsalolin duniya mai nuna cewa dalibansu na iya fuskanta,sai kuma samar da wata dama ta nuna damuwa da abubuwan da suke damun wasu.Kara gano lamurran dangane da muhimmancin daukar lokaci mai tsawo ana koyo,da kuma yadda dabarun hanyoyin koyo za su taimaka maku ku koyar ko kuma gane/gano sababbin abubuwan da suka shafi ilimi.

7.Su zama basu da nuna bambanci

Matsayinka na mai ilimi zaka kasance da alhakin koyarda dalibai masu bambancin fahimtar ita koyarwar.Idan za ka yi maganin nuna bambanci,da kuma yin adalci,akwai bukatar ka rika gwada bukatar dalibanka,ta hanyar da babu nuna wani fifiko,abinda yake bukatar kai ka ci gaba da yin bincike da kuma bada bayani kan yadda ka fahimci ko nazarci wasu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Halaye Makaranta

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya ta bayar da wa’adin ficewar dukkanin masu aikin Umrah daga kasar

Gwamnatin Saudiyya ta ayyana 1 ga watan Dhul Qada, wadda za ta yi daidai da 29 ga watan Afrilu, a matsayin ranar karshe da duk wani bako da ke kasar da zummar aikin Umarah da ya fice daga ƙasar.

Sanarwar da ma’aikatar aikin Hajji da Umarah ta Saudiyya ta fitar ta ce ta dauki matakin ne domin fara gudanar da shirye-shiryen aikin Hajji mai zuwa.

Cikin wata sanarwa, ma’aikatar ta ce ranar 15 ga watan Shawwal, da ya yi daidai da 13 ga watan Afrilu, ita ce ranar karshe da masu shiga kasar domin aikin Umrah za su daina shiga, sai dai a fita.

Ma’aikatar ta jaddada cewa duk wanda aka samu ya ci gaba da zama a kasar har ya wuce lokacin da kebe, to ko shakka babu ya saba ka’ida sannan kuma zai fuskanci hukunci.

Mahukuntan sun bukaci mutane da ma kamfanonin da ke shirya zuwa aikin Umrah da su kiyaye da waɗannan lokuta.

An kuma yi gargadin cewa duk wani jinkiri na barin mutane kasar za a dauke shi kamar karya doka.

Ta ce duk kamfanin da aka samu da ƙin bayyana mutanen da suka ki koma wa kasashensu to za a ci tararsu riyal dubu 100.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Pezeshkian: Dole ne Amurka ta tabbatar da cewa da gaske take yi a game da tattaunawa
  • Ya Kamata Lambar Yabo Ta Zama Hanyar Ƙarfafa Mana Gwuiwa – Misis Nda-Isaiah
  • Saudiyya ta bayar da wa’adin ficewar dukkanin masu aikin Umrah daga kasar
  • Kisan Janar Alƙali: Kotu ta ɗage shari’a zuwa 28 ga Mayu
  • Matsalar tsaro: Ba za mu lamunci zagon ƙasa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Faransa, Masar da Jordan sun yi kira da a tsagaita wuta cikin gaggawa a Gaza
  • Saudiyya ta sanya wa masu Umarah wa’adin ficewa daga ƙasar
  • Tsofaffin Ma’aikatan FRCN Za Su Gudanar da Zanga-zanga Kan Jinkirin Biyan Hakkokin Su
  • Mutanen da Sanƙarau ta kashe sun kai 151 — NCDC
  • Trump Ya Yada Hutunan Bidiyo Wadanda Suka Nuna Yadda Sojojin Amurka Suka Kashe Mutanen Yemen Wadanda Suke Bukukuwan Salla Karama