Sin Za Ta Buga Karin Haraji Kan Wasu Hajojin Canada Da Ake Shigarwa Kasar Bayan Kammalar Bincike
Published: 8th, March 2025 GMT
Ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ta sanar a Asabar din nan cewa, za ta kara haraji kar kaso 100 kan wasu kayayyaki da ake shigowa da su kasar daga Canada, bayan da ta kammala bincike kan batun nuna banbanci a hada-hadar cinikayya.
Harajin zai fara aiki ne tun daga ranar 20 ga watan nan na Maris, zai kuma kunshi karin kaso 100 bisa mai rapeseed, da tunkuza, da waken peas, yayin da kuma albarkatun teku, da naman alade da ake shigarwa Sin daga Canada, aka yi musu karin harajin kaso 25 bisa dari.
Mahukuntan kasar Sin sun ce matakin ya biyo bayan binciken da aka gudanar game da nuna banbanci a hada-hadar cinikayya, wanda ya tabbatar da cewa, matakan da kasar Canada ta dauka kan hajojin Sin da ake shigarwa kasar sun haifar da cikas, ga harkokin cinikayyar da aka saba gudanarwa tsakanin sassan biyu, kana sun illata halastacciyar moriyar kamfanonin kasar Sin. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Dangantaka ta yi tsami tsakanin Aljeriya da kasashen kawancen Sahel
A wani mataki na mayar da martani da nuna fishi, kasar Aljeriya ta yi wa jakadunta a kasashen Mali, da Nijar kiranye, tare da jinkirta aikewa da jakadanta a Burkina faso, bayan da kasashen guda uku na kawacen sahel suka dau irin wannan matakin domin goyan bayan Mali, bisa takadamar dake tsakaninta da Aljeriya biyo bayan kakkabo jirginta marar matuki.
Haka zalika ma’aikatar tsaron kasar Aljeriya ta sanar da rufe sararin samaniyarta ga dukkan jiragen da ke zuwa kasar Mali”, ba tare da bayar da wani karin bayani ba, wanda ke nuni da cewa jiragen farar hula na kasuwanci da kamfanonin jiragen sama na kasa da kasa su ma abin ya shafe su.
Takaddama dai ta yi zafi tsakanin Aljeriya da Mali, inda ita ma Bamako ta sanar a yammacin ranar Litinin cewa, za ta rufe sararin samaniyarta “ga dukkan jiragen saman farar hula da na soji da ke tashi ko isa Algeria.”
Amma, rufe sararin samaniyar Aljeriya bai shafi kawayen Mali wato Nijar da Burkina Faso ba, saidai Aljeriyar ta ce ba yi nadama kan yadda kasashen suka biyu suka dau irin wannan matakin ba na goyan bayan Mali ba tare da tunani ba.
A ranar Lahadi ne Kasashe uku na AES suka sanar da yin kira ga jakadun su da ke kasar Aljeriya.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar Aljeriya ta fitar, ta yi watsi da “mummunan zarge-zargen” da kasar Mali ta yi, inda ta ce Algiers ta harbo daya daga cikin jiragenta marasa matuka a kan kasarta.