NMDPRA ta ba da lasisin gina sabbin matatun mai 3 a Nijeriya
Published: 8th, March 2025 GMT
Hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Nijeriya, NMDPRA, ta bayar da lasisin kafa sabbin matatun man fetur uku a wasu jihohin ƙasar uku.
Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na X a ranar Asabar, wadda shugabanta, Farouk Ahmed ya bayyana ta nuna.
NMDPRA ta ce ta bayar da lasisin gina sabbin matatun man ne a jihohin Abia da Delta da kuma Edo.
“Za a buɗe Matatar Eghudu wadda za ta iya tace ganga 100,000 a kullum a Jihar Edo.
“Za kuma a buɗe Matatar MB wadda za ta riƙa tace ganga 30,000 a kullum a Jihar Delta, sai Matatar HIS wadda ita kuma za ta riƙa tace ganga 10,000 a kullum a Jihar Abia.”
Hukumar ta ce sabbin matatun uku idan an kammala su gaba ɗaya za su iya tace ganga 140,000 na man fetur duk rana.
Bayanai daga hukumar ta NMDPRA sun nuna cewa Nijeriya na da matatun man fetur tara, ciki har da sabuwar matatar Dangote da ke birnin Legas.
Waɗannan matatu na tace ganga 974,500 a duk rana, yayin da Matatar Dangote kaɗai ke da ƙarfin tace ganga 650,000 a kowace rana.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Matatar Dangote NMDPRA
এছাড়াও পড়ুন:
Bankin Duniya : Sake Gina Lebanon Yana Bukatar Dala Biliyan 11
Bakin duniya ya kiyasta cewa ana bukatar dala biliyan 11, domin sake gina Lebanon sakamakon barnar da hare haren Isra’ila suka haifarwa kasar.
Bangaren gidaje na Lebanon ya fi fama da matsalar, inda aka kiyasta asarar da ta kai dala biliyan 4.6, yayin da masana’antar yawon bude ido ta yi asarar dala biliyan 3.6.
“Sakamakon rikice-rikicen ya haifar da raguwa a ainihin GDP na Lebanon na 7.1 bisa dari a 2024,” in ji Bankin Duniya.
Rahoton ya kara da cewa, “Ya zuwa karshen shekarar 2024, raguwar GDP na kasar Lebanon tun daga shekarar 2019 ya kusan kashi 40%, wanda hakan ya haifar da koma bayan tattalin arziki a bangarori da dama da kuma yin tasiri ga ci gaban tattalin arzikin kasar.”
Sojojin Isra’ila sun fara kai farmaki kan sansanonin Hizbullah a kudancin Lebanon jim kadan bayan kaddamar da kisan kiyashi a zirin Gaza da aka yiwa kawanya a watan Oktoban shekarar 2023.