Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa hare-hare a kan cibiyoyin makamashin Nukliyar kasar ba zasu dakatar da ayyuka a cibiyoyin ba. Sai dai yin haka zai kara yada yaki a yankin kudancin Asiya.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Aragchi yana cewa cibiyoyin nukliya na kasar Iran suna da kekyawar kariya daga makamai.

Don haka da sauki makiyammu ba zasu cutar da cibiyoyin ba.

Ministan ya bayyana haka ne a taron kasashen musulmi na OIC wanda aka gudanar a birnin Jedda na kasar Saudiya a yau Asabar. Ya ce iran zata ci gaba da neman fahintar juna ta hanyar diblomasiyy, Amma idan sun dage zasu yi amfani da karfi to Iran a shirye take ta kare kanta, kuma bata da zabi sai hakan.

A wani bangare ministan ya bayyana cewa Iran ba ta cikin sauri wajen samar da hulda da sabuwar gwamnatin kasar Siriya.

A jawabinsa a taron na OIC Aragchi ya kawo baton kasar Falasdinu da kuma shirin Amurka na kwace Gaza daga hannun falasdinawa ta kore su zuwa kasashen Masar da Jordan. Ya yi allawadai da hakan ya kuma bayyana cewa ya sabawa dukkan dokokin kasa da kasa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Cibiyoyin Ciyar Da Masu Azumi A Dan Modi Na Garin Kafin Hausa

Gwamnatin Jihar Jigawa ta yi kira ga masu dafa abincin buda baki a karamar hukumar Kafin Hausa da su kasance masu gaskiya da adalci wajen ciyar da masu azumi a wannan watan na Ramadan.

Mai bai wa Gwamna Umar Namadi shawara kan ayyuka na musamman, Alhaji Abdulkadir Bala T.O yayi wannan kiran yayin da yake duba cibiyoyin ciyar da masu azumi na Dan Modi a cikin garin Kafin Hausa.

Alhaji Abdulkadir Bala T.O ya yaba da kokarin wasu daga cikin masu dafa abincin, yayin da ya nuna rashin jin daɗi kan yadda wasu suka karya yarjejeniyar da aka gindaya masu.

A nasa jawabin, Shugaban karamar hukumar Kafin Hausa, Alhaji Abdullahi Sa’idu Nalayi, ya tabbatar da cewar, Karamar hukumar za ta ba da dukkan goyon bayan da ya dace don gudanar da shirin cikin nasara.

Shima a jawabin sa na godiyan masu dafa abincin, Abba Darakta Kafin Hausa ya yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa kaddamar da shirin ciyar da masu azumi.

Ya kuma yi alkawarin ci gaba da kasancewa masu gaskiya da adalci don cimma manufofin da aka sanya a gaba.

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagora: Iran, Tabbas Zata Ki Amincewa Da Tattaunawa Da Kasashe Masu Girman Kai
  • Qatar Ta Ce Bata Goyon Bayan Yakin Don Warware Shirin Nukliyar Kasar Iran
  • Oficin Jakadan Iran A MDD Ya Ce Babu Wani Sako Da Suka Karba Daga Shugaban Kasar Amurka
  • Iran Da Iraki Sun Nuna Damuwa Kan Tashe-tahen Hankula A Siriya
  • Al-Houthi: Mun Baiwa Isra’ila Wa’adin Kwanaki 4 Da Ta Kawo Karshen Killace Gaza
  •  Ayatullah Khatami: Tattaunawa Da Amurka Kaskanci  Ne
  • An Bude Cibiyoyin Ciyar Da Masu Azumi A Dan Modi Na Garin Kafin Hausa
  • An Ayyana Dokar Ta-baci A Wasu Yankunan Siriya
  • Iran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Birtaniya Na Cewa Tehran Na Barazana Ga Tsaron Kasar