Leadership News Hausa:
2025-04-09@01:34:04 GMT

Girke-girkenmu Na Azumi

Published: 8th, March 2025 GMT

Girke-girkenmu Na Azumi

Ruwan kanwa wani ruwa ne da akeyiwa mai azumi yanada dadi sosai sannan idan mai azumi ya sha bayasa kasala yana warware cikin ko hanji cikin mutum zance, idan mai azumi yasaba da shan ruwan kanwa duk randa baisha ba bazai taba jin dadi ba.

Ya ake ruwan kanwa?

Da farko za ki samu gero sai a surfashi a cire masa dusa sannan a wankeshi a shanyashi yasha iska wato ya bushe sosai sai kidan soyashi yayi kanshi haka sannan ki zuba masa kayan kamshi citta, kanunfari, musuru, saiki bayar a nikamiki shi yayi laushi sosai kamar na kunu kizo ki shanyashi ya bushe sai ki ajiyeshi duk idan zaki dama saiki diba ki zuba a wani dan bokiti haka sai ki damashi da dan ruwan kanwa dama kin dora ruwa a wuta kamar de yadda zakiyi kunu idan ruwa ya tafasa saiki kashe shi kidan barshi yasha iska saboda karyazama kunu saiki zuba sannan ki zuba can suga haka saiki ajiyeshi haka ake shanshi da dumi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Faransa, Masar da Jordan sun yi kira da a tsagaita wuta cikin gaggawa a Gaza

Shugabannin kasashen Faransa da Masar da kuma Jordan sun fitar da wata sanarwa ta hadin gwiwa inda suka bukaci a tsagaita bude wuta cikin gaggawa a Gaza, tare da sukar Isra’ila kan gazawarta wajen tabbatar da ayyukan jin kai a zirin.

Kiran tsagaita wuta ya nuna bukatar samar da agajin jin kai cikin gaggawa a Gaza kuma ya nuna damuwar da kasashen duniya ke ci gaba da yi kan tashe-tashen hankula da rikicin jin kai a Gaza.

Haka kuma sanarwar wadannan kasashe uku ta nuna muhimmancin hanyar diflomasiyya na samun zaman lafiya da kwanciyar hankali.

A baya dai shugaba Macron ya nuna adawarsa da mamaye yankunan Falasdinawa da Isra’ila ta yi.

Macron ya kuma kira sabbin hare-haren da Isra’ila ta kai a yankin bayan rugujewar yarjejeniyar tsagaita bude wuta a tsakiyar watan Maris da cewa wani babban koma baya ne.

Sarki Abdallah na biyu na Jordan, shugaban Faransa Emmanuel Macron, da shugaban Masar Abdel Fattah el-Sisi na Masar sun bayyana cewa, “Dole ne a dakatar da yakin Gaza duba da bala’in  da ya haifar a yanzu.

Tashin hankali, ta’addanci, da yaki ba za su iya samar da zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya ba.

Sanarwar ta yi nuni da bukatar gaggawa na kara kai kayan agaji a Gaza, inda tuni aka fara samun matsalar yunwa, da kare hukumomin Majalisar Dinkin Duniya da ma’aikatan jin kai da ke aiki a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Boko Haram na sake ƙwace ikon wasu yankuna a Borno — Zulum
  • Trump Yayi Barazanar Karawa China Kashi 50% Na Kudaden Fito A Dai-Dai Lokacinda Suka Shiga Tsakiyar Yakin Tattalin Arziki
  • Sojoji 2 Da ’Yan Ta’adda Da Dama Sun Rasu A Wani Gumurzu A Borno
  • Faransa, Masar da Jordan sun yi kira da a tsagaita wuta cikin gaggawa a Gaza
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 4, Sun Sace 45 A Katsina
  • Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 30 a Kongo
  • Ambaliya Ta Hallaka Mutum 30 A Birnin Kinshasa Na Jamhuriyar Demokradiyar Congo
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Rika Bayar Da Maganin Hawan Jini Da Siga Kyauta
  • An Kori Jirgin Ruwan Japan Da Ya Shiga Yankin Ruwan Kasar Sin Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Burtaniya Ta Soki Gwamnatin Netanyahu Kan Hana ‘Yan Majalisarta Biyu Shiga Cikin Isra’ila