HausaTv:
2025-04-09@05:50:42 GMT

Qatar Ta Ce Bata Goyon Bayan Yakin Don Warware Shirin Nukliyar Kasar Iran

Published: 8th, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Qatar Mohammad Bin Abdurrahman Al-Thani, ya kara nanata matsayin kasar na kin duk wani yaki kan shirin Nukliyar kasar Iran, ya kuma yi kira ga Amurka da Iran su warware wannan matsalar ta ruwan sanyi. Ko hanyar diblomasiyya.

Kafin haka dai JMI ta sha nanata cewa shirinta na makamashin na zaman lafiya ne.

Sannan don haka ne ta amince ta kulla yarjeniyar shirin nukliya ta zaman lafiya  da manya manyan kasashen duniya, a shekara ta 2015 daga ciki har da kasar Amurka. Amma shugaban kasar Amurka na lokacin Donql Trump ta fidda kasar daga yarjeniyar sannan ta dorawa kasar takunkuman tattalin arziki mafi muni don tursasa mata ta sake zama don sabuwar tattaunawa da ita.

Mohammed bin Abdulrahman Al Thani yace “akwai bukatar kasashen Iran da Amurka su fahinci juna a cikin wannan batun” sannan ya sake nanata cewa Qatar bata goyon bayan yaki. Sannan daga karshe yace matsalar nukliyar kasar Iran ta zama abinda damuwa ga dukkan kasashen yankin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran da Amurka zasu fara tattaunawa a Oman ranar Asabar

Jamhuriyar musulinci ta Iran, ta bayyana cewa za ta fata tattaunawa wacce ba ta kai tsaye ba da Amurka a ranar Asabar mai zuwa a kasar Oman.

Ministan harkokin wajen Iran din ne Abbas Araghchi ya bayyana hakan a shafinsa na ‘’X’’ a safiyar Talata.

“Iran da Amurka za su gana a Oman ranar Asabar don tattaunawa mai zurfi, inji ” Araghchi.

“Wannan wata dama ce, kuma kwallo yana hannun Amurka,” ta nuna da gaske ta ke in ji shi.

Kalaman Araghchi na zuwa ne bayan shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa Amurka da Iran suna tattaunawa kai tsaye, bayan ganawa da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu a Washington.

Shugaban na Amurka ya ce tattaunawar da za a yi tsakanin Washington da Tehran za ta kasance a matsayi mai girma.

A cikin Ofishin Oval na Fadar White House, Trump ya kuma ce: “Muna da babbar ganawa a ranar Asabar (da Iran), kuma muna mu’amala da su kai tsaye… Kuma watakila za a cimma yarjejeniya, hakan zai yi kyau.” Inji shi.

Iran dai ta sha nanata cewa a shirye ta ke ta shiga tattaunawa da Amurka amma ba bisa matsin lamba ko barazana ba.

A baya bayan nan dai shugaban Amurka ya yi barazarar amfani da bama-bamai kan Iran, idan batayi amfani da damar tattaunawar ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump Yayi Barazanar Karawa China Kashi 50% Na Kudaden Fito A Dai-Dai Lokacinda Suka Shiga Tsakiyar Yakin Tattalin Arziki
  • Gwamnatin Kasar Aljeriya Ta Dakatar Da Zirga-Zirgan Jiragen Saman Kasar Zuwa Kasar Mali
  • Iran da Amurka zasu fara tattaunawa a Oman ranar Asabar
  • Sharhin Bayan Labarai: Zanga-Zanga A Kasashen Larabawa Ta Goyon Bayan Falasdinaw A Gaza
  • Kasar Sin Ta Nanata Kudurinta Na Ci Gaba Da Bude Kofa Yayin Wani Taro Da Kamfanonin Amurka 
  •  Kasashen Iran, Rasha Da China Za Su Yi Taro A Moscow Domin Tattauna Batutuwa Da Dama
  • Cin Zali Ba Zai Iya Hana Kasashen Afirka Ci Gaba Ba
  • Iran : kasashen turai sun tafka kure na tarihi, ta hanyar goyan bayan Isra’ila
  • NAJERIYA A YAU: Mene ne Tasirin Shirin NYSC Bayan Shekaru 50 Da Kafa Shi?
  • Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya