Qatar Ta Ce Bata Goyon Bayan Yakin Don Warware Shirin Nukliyar Kasar Iran
Published: 8th, March 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Qatar Mohammad Bin Abdurrahman Al-Thani, ya kara nanata matsayin kasar na kin duk wani yaki kan shirin Nukliyar kasar Iran, ya kuma yi kira ga Amurka da Iran su warware wannan matsalar ta ruwan sanyi. Ko hanyar diblomasiyya.
Kafin haka dai JMI ta sha nanata cewa shirinta na makamashin na zaman lafiya ne.
Mohammed bin Abdulrahman Al Thani yace “akwai bukatar kasashen Iran da Amurka su fahinci juna a cikin wannan batun” sannan ya sake nanata cewa Qatar bata goyon bayan yaki. Sannan daga karshe yace matsalar nukliyar kasar Iran ta zama abinda damuwa ga dukkan kasashen yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Gabatar Da Tayin Shiga Tsakanin Don Sasanta Indiya Da Pakisatan
A dai-dai lokacinda kasashen Indiya da Pakisatn suke tada jijiyoyin wuta kan wani harin ta’addanci da ya kai ga mutuwar mutane 27 masu yawon shakatawa a yankin Kashmir na kasar Indiya, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya gabatar da tayin shiga tsakani don dai-daita tsakanin kasashen biy.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka, a shafinsa na X, ya kuma kara da cewa Iran tana da dangantaka mai karfi tsakaninta da kasashen biyu, kuma makobta ne kuma yan uwa wadanda suke da tsohuwar dangantaka ta al-adu a tsakaninsu na karnuka, ba za muyi kasa a guiwa wajen sasantasu ba, idan sun bamu wannan damar.
A cikin makon da ya gabata ne wasu yan bindiga suka bude wuta kan wasu maso yawan shakatawa a yankin Kashmir na kasar Iran inda mutane 27 suka mutu. Gwamnatin Undiya tana zargin Pakistan da hannu dumu-dumu a cikinsa, a yayinda gwamnatin kasar Pakisatan ta musanta hakan ta kuma yi allawadai da harin. Amma ta kara da cewa idan indiya ta kuskura ta yi amfani da makami a kanta to zata rana.
A daren jamm’an da ta gabata dai bangarorin biyu sun kai ga musayar wuta a tsakaninsu a kan iyakokin kasashen biyu.
Ministan ya bayyana cewa kasar zata yi amfani da ofisoshin jakadancin kasashen biyu a Islamabad da kuma New Delhi don shiga tsakanin su idan sun amince da hakan.
Kasashen indiya da Pakistan dai sun dade suna takaddama kan mallakar Yankin Kashmir kuma sun sha shiga yaki saboda hakan.