Qatar Ta Ce Bata Goyon Bayan Yakin Don Warware Shirin Nukliyar Kasar Iran
Published: 8th, March 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Qatar Mohammad Bin Abdurrahman Al-Thani, ya kara nanata matsayin kasar na kin duk wani yaki kan shirin Nukliyar kasar Iran, ya kuma yi kira ga Amurka da Iran su warware wannan matsalar ta ruwan sanyi. Ko hanyar diblomasiyya.
Kafin haka dai JMI ta sha nanata cewa shirinta na makamashin na zaman lafiya ne.
Mohammed bin Abdulrahman Al Thani yace “akwai bukatar kasashen Iran da Amurka su fahinci juna a cikin wannan batun” sannan ya sake nanata cewa Qatar bata goyon bayan yaki. Sannan daga karshe yace matsalar nukliyar kasar Iran ta zama abinda damuwa ga dukkan kasashen yankin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Oficin Jakadan Iran A MDD Ya Ce Babu Wani Sako Da Suka Karba Daga Shugaban Kasar Amurka
Ofishin jakadancin JMI dake MDD a birnin New York na kasar Amurka ya bada sanarwan cewa bai karbi wani sako daga shugaban kasar Amurka Donal Trump ba.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakoto Jaridar Axios ta Amurka na cewa Shugaban kasar Amurka ya aikawa jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Ayatullahi Khaminae wasika, inda a ciki yake kiransa zuwa tattaunawa da Amurkan a kan shirin makamashin Nukliyar kasar Iran.
Har’ila yau shugaban ya bayyana haka wa tashar talabijin ta Fox news. Iran dai ba ta son tattaunawa kai tsaye da Amurka saboda rashin gaskiya a cikin al-amuransu. Musamman shi Donal Trump, sabo da shine ya fidda kasarsa daga yarjeniyar JCPOA tun farko sannan ya dage sai ta sake tattauna da Iran sabowayar yarjeniya.
Kafin haka dai jagoran ya bayyana cewa, tattaunawa da Amurka a dai dai lokacinda take takurawa kasar da takunkuman tattalin arziki, ba zai yu ba, saboda daukan kaskanci ne wanda bai dace da JMI.
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiya ya jaddada goyon bayansa ga ra’ayin Jagoran dangane da tattaunawar.