Aminiya:
2025-04-29@14:42:27 GMT

WHO za ta bai wa Nijeriya magungunan cutar kuturta

Published: 8th, March 2025 GMT

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce za ta aika da magungunan cutar kuturta zuwa Nijeriya a ƙarshen makon nan.

Wannan dai na zuwa ne bayan jinkirin da aka samu na gwaje-gwajen da hukumar ke gudanarwa, lamarin da ya jawo dubban masu fama da cutar ciki har da yara ba su samu magungunan da suka kamata na kare cutar ba.

Mun kama ’yan bindiga da suka yi kutse a Kano — ’Yan sanda NMDPRA ta ba da lasisin gina sabbin matatun mai 3 a Nijeriya

Kakakin hukumar ta WHO ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters cewar, an samu ƙarancin maganin cutar ta kuturta a Nijeriya.

Ya ce hukumar ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta miƙa buƙatar ganin an samu izinin shigar da maganin cikin ƙasar akan lokaci, kuma a watan Janairu aka amince da hakan.

Nijeriya wadda ita ce ƙasar Afirka da ta fi yawan jama’a na bayar da rahoton samun aƙalla mutum 1,000 da cutar kuturta a duk shekara, wadda cuta ce da ke kama fatar jiki da jijiyoyi da idanu.

Ana iya magance cutar bayan shan magani na wani lokaci, amma idan ba a shan magani, cutar na ƙaruwa, idan take jawo gyambo da kuma nakasa kamar makanta da shanyewar rabin jiki.

Haka kuma, masu fama da cutar na fuskantar hantara da tsangwama a cikin al’umma.

Sai dai magungunan da Nijeriya take da su na cutar sun ƙare a farkon shekarar 2024 sakamakon jinkirin da aka samu na sabbin dokokin cikin gida da aka samar na gwaje-gwaje kan magungunan da ake shigar da su cikin ƙasar.

Jinkirin wanda ya jawo wahalhalu a Nijeriya, misali ɗaya ne daga ake samu a tsarin duniya wanda ke faruwa a ƙasashe da dama waɗanda suka haɗa da Indiya da Brazil da Indonesia a ‘yan shekarun nan, kamar yadda wakili na musamman na Majalisar Ɗinkin Duniya kan cutar kuturta ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Ƙididdigar WHO ta nuna cewa Nijeriya na ɗaya daga cikin ƙasashe 12 da ke bayar da rahoton kamuwa da cutar inda ake samun tsakanin mutum 1,000 zuwa 10,000 a duk shekara masu kamuwa cutar, bayan Brazil, Indiya da Indonesia.

Kowace ƙasa tana buƙatar allurai na kuturta, wanda magani ne na kafso da ake amfani da shi na tsawon watanni 12, daga WHO kowace shekara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya cutar kuturta

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin faɗuwar farashin kayan abinci a kasuwannin Arewa

A shekarar bara, ’yan kasuwa, musamman masu hadahadar kayan abinci da na amfanin gona a Nijeriya, kakarsu ta yanke saka, saboda tashin gwauron zabon da kayan a kasar.

Galibin wadannan amfanin gona na kasuwanci ana fitar da su zuwa kasashen a duniya.

Hukumar Bunkasa Fitar da Kayayyaki ta Nijeriya (NEPC) ta sanar a watan Agusta na shekarar ta 2024, cewa Najeriya ta samu gagarumin ci-gaba a fannin fitar da kayayyaki da ba na man fetur ba a watanni shidan farkon shekarar, inda ta samu kudin shiga kimanin dala biliyan 2.7.

Yawan bukatar kayan a kasuwannin duniya ya kawo hauhawar farashin kayan abinci na yau da kullum da amfanin gona na kasuwanci.

An kuma yi hasashen cewa farashin zai ci gaba da tashi a shekarar 2025.

A lokacin da farashin ke hauhawa, ’yan kasuwa da dama sun zuba jari mai yawa, musamman a harkar ridi da waken suya, da fatan samun gagarumar riba idan bukatar kayayyakin ta karu a kasuwannin duniya.

Sai dai a cikin wani yanayi mai matukar daure kai, sai ga shi farashin na ta faduwa warwas, musamman a Arewacin kasar nan.

Ma’aunin Farashin Kayayyaki (CPI) ya nuna an samu saukar farashin da kimanin kaso 25 cikin 100, daga N87 zuwa N65 a cikin watan Maris din 2025, kamar yadda kamfanin mai zaman kansa na farko a Nijeriya da aka ba lasisin hada-hadar musayar kudaden kayayyaki, AFED, ya bayyana.

Alhaji Abdullahi Usman, Shugaban Kamfanin kayayyakin abinci na Mumin Foods Ltd, wanda a cewarsa ya fi shekara 30 yana kasuwancin ridi, ya bayyana cewa faduwar farashin na da nasaba da yadda bukatar amfanin gonar da ake nomawa a Nijeriya ta ragu matuka a kasuwannin duniya.

Ya ce, sai sai abin takaici, tun bayan da bukatar kayayyakin ta karu, ’yan kasuwa da dama sun rika fito da kudade suna sayen kayan, ciki har da kayan abinci.

Dan kasuwar ya bayyana cewa saukar farashin ya kara nuna yadda kasashe suka dage wajen noma abin da za su ci, shi ya sa kasuwannin Nijeriya suka cika suka batse da kayayyaki, wanda hakan ya sa ala tilas farashinsu ya fadi.

Ya ce “Mutane sun fito da mazajen kudade wajen sayewa tare da boye kayayyakin, duk da wasu ’yan kasashen waje na hankoron sayen amfanin gonar da ake nomawa a Nijeriya musamman kasancewar sun yi amanna da cewa na asali ne ba wanda aka gurbata da sinadarai wajen noma su ba.

“Da farko dai alkaluma sun nuna komai na tafiya yadda ake bukata, sai mutane suka ci gaba da karuwa.

“Sai dai abin takaici, sai bukatar wadannan kayan daga kasashen ta ragu sosai, wanda hakan ne ya tilasta faduwar farashin kayayyakin amfanin gonar,” in ji shi.

Bayanai sun nuna cewa kilo ɗaya na ridi wanda a bara aka sayar da shi N2,300, a yanzu ana sayar da shi N1,600.

Sai kuma kilo daya na zobo wanda shi kuma a bara yake 2,300, a bana ya dawo naira1,500.

Wasu majiyoyi a harkar hada-hadar amfanin gona sun ce ana hasashen akwai yiwuwar farashin ya ci gaba da faduwa yayin da kasashen waje ke ci gaba da rage yawan bukatar kayan na Najeriya.

Haka kuma an yi amannar cewa faduwar farashin kayan abincin zai kawo sauki ga iyalan da ke rayuwar hannu-baka-hannu-kwarya na dan wani lokaci, ba lallai ta ci gaba da zama a haka ba.

Bugu da kari, mutanen da ke sayar da wadannan kayayyakin ba su cika yin asara ba kasancewar suna da inda za su ajiye su har zuwa lokacin da farashin zai musu inda suke so.

Masana tattalin arzikin amfanin gona kuma na hasashen cewa dawowar Indiya fitar da kayan da take nomawa zuwa kasashen ketare, zai sa yawan bukatar kayayyakin ta ragu a duniya, wanda hakan zai iya sawa farashin ya dada sauka, na daya daga cikin dalilan da suka jawo karyewar farashin a Najeriya a ’yan watannin nan.

Alhaji Abdullahi Usman, shugaban Mumin Food Limited, ya ce karancin masu sayan kayan masarufin Nijeriya a cinikayyar kasa da kasa na da alaka da faduwar kayan masarufi a cikin kasa Nijeriya.

Ya kara da bayanin cewa, “Abin takaici, yadda bukatun ’yan Nijeriya suke karuwa na sayen kayan masarufi, wasu daga cikin ’yan kasuwa sun saye kayan masarufin da kayan gonar, kara da cigaban da aka samu kwanan nan wanda ya ba wa ’yan kasashe dama su inganta amfanin gonarsu kuma su rage shigowa da kayan ketare, ya sa farashin wasu kayan masarufi ya sauka.

“Mutane da dama suna ajiye kayan masarufi musamman a lokacin da wasu kasashe suka nuna suna bukatar wani nau’i na kayan masarufi daga Nijeriya, saboda kayan masarufin Nijeriya ba su da sinadaran zamani.

“Amma cikin babu zato sai bukatun wadannan kasashe suka yi kasa wanda hakan ke da alaka da saukar farashin kayan masarufin.

“Bugu da kari, faduwar farashin yana kawo rangwamen wucin gadi ga masu sayen dai-dai wanda suke a gida.

“Amma masu ta’ammali da kayan masarufi abin ba ya shafar su, saboda suna da hanyar ajiye kayan har zuwa wani lokacin da ya yi musu,” kamar yadda dan kasuwan ya bayyana.

Masana noma da tattalin arziki sun tabbatar da rahoton cewa kasar Indiya ta dawo fitar da kayan masarufi zuwa kasashen ketare, a maimakon sayowa daga can, wanda hakan ke nuni da cewar za a iya samun faduwar farashinsu a ƙasashen da suke sayar wa da Indiya kaya.

Daga wani masanin tattalin arziki daga Kwalejin Ilimi na Sa’adatu Rimi da ke Kano, Mallam Hassan Ali, “Darajar naira da kuma dalar Amurka na taka rawar gani wajen saukaka wa al’amuran shigo da kaya.

“Haka kuma, Babban Bankin Kasa (CBN) ya ce hadahadar canjin naira zuwa dalar Amurka yana yawo tsakanin N1,478 d kuma N1,551 daga watan 1 na Janairu, 2025 har zuwa yanzu.”

Ya bayyana cewa, “Wannan na nuni da faduwar sama da kaso 8% daga N1,688 da yake a kididdigar wasu watanni na shekarar 2024.

Haka zalika, yanayin lokaci kusan shi ne kashin bayan hawa da faduwar farashi a kasuwar kayan masarufi, saboda lokacin shuka da girbi yana shafar yanayin hadahadar kayan abincin da kuma farashinsu.

Kusan akwai hasashen cewa makonni bayan girbe amfanin gona (lokacin kaka) farashin kayan abinci da sauran kayan gona yana faduwa kasa saboda yawan saya da kuma fitar da su da manoma ke yawan yi a wannan lokacin.”

A Jihar Kano an samu rohoton cewa ana samun sauye-sauyen tashin farashin kayayyakin masarufi da dama, musamman canjin yanayi da ake samu da kuma yadda ake samar da kayayyakin da suka shafi amfanin gonar.

Wani manomin ridi daga Jihar Jigawa, Alhaji Sagir Bello Black, ya sanar cewa a lokutan girbi farashin kayayyaki yana raguwa sakamakon yawan wadatar kayayyakin masarufi a kasuwa, sannan kuma yakan tashi a lokacin rani saboda karancin kayayyakin.

Ya kara da cewa, gazawar samar da isashen kayayyakin da ’yan kasuwa ke bukata irin na baya saboda rashin ruwan sama ko yawan ruwan sama, da tashe-tashen hankula da rashin tsaro, na haifar da hauhawar farashin kayayyakin amfanin gona.

Alhaji Aminu Gumel, wani dan kasuwar ridi wanda a cewarsa ya shafe sama da shekara 30 yana kasuwancin ridi, ya bayyana cewa ya sayi kayayyaki na miliyoyin nairori don fitarwa, amma abokan kasuwancinsa na kasashen waje ba su biya ba tukuna, sabanin yadda al’amura suka kasance a shekarun baya.

Alkasim Idris Ajingi, manomin citta, ya kara da cewa, “A shekarar 2023 Nijeriya ta fuskanci karancin noman citta sakamakon cutar kwari da ta lalata kusan kashi 70% na amfanin gona.”

Ya kara da cewa, “Wannan annoba ta kawo raguwar wadata da samuwar kayayyakin wanda ya kawo hauhawar farashin citta da ninki shida na tsawon shekaru daga N50,000 zuwa N300,000 a kowane buhu.

Ya kara da cewa, “Lokacin da manoma ke fuskantar matsalolin noma a wannan lokacin kuma kayayyaki ke raguwa shi ya sa farashin kaya dole ne ya tashi.”

Kayayyakin Nijeriya sun samu karɓuwa a duniya

Kayan masarufin Nijeriya sun samu karbuwa a kididdigar kasuwar duniya.

Misali, likafar kasuwar waken suya a kasar ta ci gaba, saboda hana shigowa da shi a 2023/2024.

Bincike ya nuna yadda matakin ya taka rawar gani wajen karuwar bukatar ’yan Nijeriya a kan waken suya.

Rahoto ya bayyana cewa waken suyar da ake fitarwa daga Nijeriya ya yi tashin gwauron zabo da sama da 1000%.

Haka ne ya sa farashin yake karuwa a cikin gida da kasuwannin kasa da kasa ya karu daga dala miliyan 10.8 a 2022, zuwa dala miliyan 201 a 2023, da farashin cikin gida wanda ya ƙaru da sama da 1 million a kowane awo.

Bugu da kari, bincike ya tabbatar da cewa kilo din waken suya an sayar da shi akan N1,300 a shekarar da ta wuce, kuma ana sayar da shi a kan N7,500 a yanzu.

Mista Chucks Idowu, wani attajiri da ke kasuwancin waken suya ma kasa da kasa, ya ce kasashen da suke bukatar waken suyar daga Nijeriya su ma suna noma tasu, shi ya sa bukatarta a kasuwar duniyar yake raguwa.

Ya kara bayyana cewa, “Karin farashin waken suyar, a shekarar da ta gabata ya sa mutane da dama suka saya suka ajiye, kuma yanzu farashin ya fadi, dole suka fito da shi don sayarwa a halin da kasuwa take a yanzu ko ba don komai ba, za su so su ci abinci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar
  • Amurka Ta Ce: Shugaban Rikon Kwarayar Siriya Al-Julani Ya Yi Alkawarin Cewa Ba Zai Cutar Da Tsaron Isra’ila Ba
  • Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje
  • Dalilin faɗuwar farashin kayan abinci a kasuwannin Arewa
  • Kasashen Duniya Sun Yi Ta AiIka Tallafi Bayan Fashewar Bandar Abbas
  • Gwamnan Babban Bankin Sin: Harajin Amurka Ya Jefa Kasuwanni Da Kasashe Masu Tasowa Cikin Hadari