Leadership News Hausa:
2025-04-09@00:34:00 GMT

Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan

Published: 9th, March 2025 GMT

Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan

Sunana Zainab Zeey Ilyas Jihar Kaduna:

Muhimmancin sadaka na da yawa baya ga kariya da take yi, sadaka tana hana bambancin da ake yi tsakanin mai kudi da kuma talaka, sadaka tana hada kan al’umma musulmi guri daya, tana taimakawa marayu, masu takaba da manya wadanda suka manyanta wajen nuna musu cewar suma suna da gata, tana kuma kusanto mutum da Allah ta’alla.

Wadanda ya kamata a bawa sadaka; Marayu, iyalai masu karamin karfi, masu takaba, ‘yan gudun hijra, dalibai da sauransu. Hanyoyin bada sadaka na da dumbin yawa kamar; bada sadaka ta hanyar bada kudi, yinta ta hanyar dauke abu daga kan hanya wanda zai cutar da dan’Adam, hada kungiya ko kirkirar kungiya ko bada gudunmawa a kungiyar taimakon al’umma, ko bada kaya a madadin yardar su, bada kayan abinci a dafe ko danye da dai sauransu. Shawara ga marasa yin sada shi ne su rinka yi da kadan-kadan domin kuwa sadaka ba ta yin yawa ba ta kadan, komai kankantar sadakar da kayi sadaka ce indai har da zuciya da ka bada ita, sannan su san amfanin sadaka, su san hanyoyin sadaka.

 

Sunana Aminu Adamu, Malam Maduri A Jihar Jigawa:

To magana ta gaskiya muhimmancin sadaka a rayuwar dan’adam musamman musulmi tana da yawa, musamman sadakar da aka yi domin Allah, domin tana taimakawa wajen karbar addu’a, kawar da masifu dama karin budi a fannoni da dama na rayuwa don haka muhimmancin sadaka ya fi gaban kidayawa. To magana ta gaskiya wadanda ya kamata a bawa sadaka sunada yawa ,kamar; maskinai, masu karamin karfi, matafiya dama ‘yan’uwa makusanta. To hanyoyin yin sadaka sunada dama kamar; ciyarwa, samar da ruwan sha, rabawa al’umma kudi ko kayan abinci dama fadawa mutane kyakkyawar magana domin ita ma sadaka ce, don sadaka tana da nau’oi da yawa. To magana ta gaskiya kin yin sadaka ga masu hali tamkar tauye Kai ne, domin yin sadaka taimakon kai ne, domin ita sadaka tana bude kofofin alkairai da dama ga masu yin ta, don haka ya kamata mu daure mu rika yin sadaka daidai karfin mu domin za ta zama budi a gare mu, Allah ya bamu ikon yin sadaka domin Allah.

 

Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Jihar Kano Rano LGA:

Tana maganin Masifa da wani iftila’ in da bai zo wa bawa ba.

Muskinai musamman wadanda ba su da lafiyar da za su iya neman na kansu wadanda sai an taimaka musu ko sun fito bara suke samun abin da za su ci. Hanyoyin yinta suna da yawa amma wacce Allah ya fi so ita ce; wadda za ka yi da hannun dama hagun ba ta sani ba. Gaskiya shawarata a gare su su daure su rika ko babu yawa kuma ayi ta domin Allah badon ayi a burge wasu ba, sabida koda ayyukan da mamaci yake mora bayan mutuwarsa akwai sadaka a cikinsu to kun ga kuwa ita sadaka ba karamin aikin lada bace gaskiya. Allah ya sa mu dace.

Sunana Muhammad Isah Zareku Miga A Jihar Jigawa:

Sadaka magani ce, waraka ce, kuma kariya ce daga dukkan cututtuka Sadaka garkuwa ce daga sharrin arayi, ko gobara, da dai sauran su. Sadaka na daya daga samun sauki da waraka daga cuta ko wacce irin matsala. A cikin hadisin manzon Allah (S.A.W) an ambaci cewa; sadaka na iya kawar da bala’i kuma tana warkar da cututtuka. Shawara idan mutum yana sadaka tana hana bala’i, sadaka na jawo albarka, sadaka na tsarkake rai da kuma dukiya, sadaka nasa Allah ya saukaka wa mutum.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ramadam

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da hare-haren Filato, sun nemi a yi adalci

Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF), ta yi Allah-wadai da harin da aka kai wasu ƙauyuka na Ƙaramar Hukumar Bokkos da ke Jihar Filato.

Ƙauyukan da abin ya shafa sun haɗa da Ruwi, Manguna, Daffo, Josho da Hurti.

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Taraba Fasinja ya yi ƙoƙarin buɗe ƙofar jirgi a sararin samaniya

Shugaban ƙungiyar kuma gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana waɗannan hare-hare a matsayin rashin hankali da tausayi.

Ya ce an kashe mutane da dama ciki har da mata da yara, yayin da wasu da dama suka jikkata.

Ya ƙara da cewa irin waɗannan hare-hare na barazana ga zaman lafiya da haɗin kan yankin Arewa.

A wata sanarwa da kakakinsa, Ismaila Uba Misilli, ya fitar a Gombe, Gwamna Yahaya ya bayyana jimaminsa game da wannan mummunan lamari.

Ya jajanta wa iyalan waɗanda abin ya shafa da kuma gwamnatin Jihar Filato da al’ummarta baki ɗaya.

Gwamnan ya bayyana damuwarsa kan yadda rikici ke ci gaba da addabar yankunan karkara, musamman yadda ake yawan zubar da jinin bayin Allah.

“Rayuwar ɗan Adam abu ce girma da ba za a yi wasa da ita ba. Waɗannan mugayen hare-hare da ake kai wa mutane abin Allah-wadai ne, kuma dole ne a dakatar da su,” in ji Gwamna Yahaya.

Ya yaba da matakin gaggawa da Gwamna Caleb Mutfwang na Jihar Filato, ya ɗauka bayan faruwar lamarin, da kuma ƙoƙarin jami’an tsaro wajen shawo kan rikicin.

Sai dai ya buƙaci jami’an tsaro da su ƙara himma wajen kamo waɗanda suka aikata wannan aika-aika tare da tabbatar da cewa an hukunta su.

Gwamna Yahaya ya kuma buƙaci a ƙara ƙoƙarin wayar da kan jama’a kan zaman lafiya, haƙuri da fahimtar juna a tsakanin al’umma, musamman tsakanin manoma da makiyaya.

Ya jaddada ƙudirin gwamnonin Arewa na aiki tare wajen kawo ƙarshen rikice-rikice, ta hanyar ƙarfafa tsaro, tattaunawa da aiwatar da manufofin da za su kawo zaman lafiya da haɗin kai.

Ya kuma buƙaci shugabannin al’umma, ƙungiyoyin addinai da na fararen hula da su tallafa wa gwamnati ta hanyar yaɗa sakon zaman lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Saudiyya ta bayar da wa’adin ficewar dukkanin masu aikin Umrah daga kasar
  • Kasar Sin Na Shirin Gaggauta Karfafa Karfinta A Bangaren Aikin Gona
  • Saudiyya ta sanya wa masu Umarah wa’adin ficewa daga ƙasar
  •  Kasashen Iran, Rasha Da China Za Su Yi Taro A Moscow Domin Tattauna Batutuwa Da Dama
  • Matakin Sin Na Karfafa Takaita Fitar Da Abubuwa Masu Alaka Da Ma’adanan “Rare Rarth” Na Nuni Ga Aniyarta Ta Kare Tsaron Kasa
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Rika Bayar Da Maganin Hawan Jini Da Siga Kyauta
  • Zanga-zangar da za mu yi babu gudu babu ja da baya — Take It Back
  • Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da hare-haren Filato, sun nemi a yi adalci
  • Mene ne matsayin azumin Sitta Shawwal a Mazhabar Malikiyya (2)