HausaTv:
2025-04-08@22:17:35 GMT

Tashe-tashen Hankula Na Ci Gaba Da Yin Sanadin Rayuka A Siriya

Published: 9th, March 2025 GMT

Rahotanni daga Siriya na nuni da cewa gomman mutane ne sukayi shahada a sabon rikicin da ya barke a baya baya nan a wasu sassan kasar.

Majiyoyin cikin gida na kasar sun tabbatarwa da tashar Al-Mayadeen cewa, a safiyar Asabar an yi ta kashe-kashe a kauyuka da garuruwa da dama a yankunan karkarar Latakia, Tartous da kuma Hama.

Majiyar ta yi nuni da cewa an yi wani kisan kiyashi a kauyen Al-Sanobar da ke gundumar Jableh.

A cewar wani rahoto na wucin gadi, an kashe mutane 72.

An tabbatar da mutuwar wasu mutane 10 a kauyen Harisoun da ke cikin karkarar Baniyas a cikin gundumar Tartous.

A sa’i daya kuma, kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasar Syria (SOHR) ta yi nuni da cewa mazauna al’ummar Alawite na cikin fargabar da ke da alaka da yiwuwar kisan kiyashi a kansu daga kungiyoyi masu dauke da makamai masu alaka da gwamnatin al-Jolani.

Kungiyar kare hakkin bil adama ta Syria ta tabbatar da cewa an raba dimbin iyalai daga kauyuka da garuruwan da ke gabar teku, ba tare da wani bayani kan makomar wadannan iyalai ba.

Majiyoyin cikin gida sun ruwaito wa Al-Mayadeen cewa an kashe fararen hula fiye da 400 a kisan kiyashi da kisa a gabar tekun Siriya.

Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama a Syria ta bayar da rahoton cewa, sama da fararen hula 300 ne aka kashe tun daga ranar alhamis a yayin wani samame da suka kan magoya bayan tsohon shugaban kasar Bashar al-Assad a yankin gabar tekun yammacin kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Fasinja ya yi ƙoƙarin buɗe ƙofar jirgi a sararin samaniya

Jirgin da ke ɗauke da mutane sama da 200 daga Bali a ƙasar Indonesia zuwa Ostireliya, ya yi juyawar dole bayan wani fasinja ya yi yunƙurin buɗe ƙofarsa yayin da jirgin kamfanin Jetstar ke shawagi a tekun Indiya.

“Mun samu wani jirgin sama ya koma Denpasar (filin jirgin sama na Bali) a daren Talata bayan wani ruɗaɗen fasinja ya yi yunƙurin buɗe ɗaya daga cikin kofofin jirgin kuma ya ci zarafin ma’aikatanmu,” a cewar wata sanarwa da kamfanin jirgin sama ya fitar game da lamarin a daren Litinin, 31 ga Maris.

Ɓarawo ya haɗiye ɗan kunnen Naira biliyan ɗaya Tsohon Gwamnan Oyo Olunloyo ya riga mu gidan gaskiya

Hukumomin yankin Bali ne suka fitar da fasinjan daga cikin jirgin.

A wani bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta, wata mata a bayan jirgin ta yi nasarar daga hannun kofar kafin sakon gargadi ya sanar da ma’aikatan jirgin, in ji kyaftin a amsa kuwwa jirgin (sifika).

Bayanai daga shafin sa ido na jirgin na Flightradar24 sun nuna cewa jirgin ya bi ta kan tekun Indiya kimanin sa’a guda a cikin jirgin.

Jetstar bai bayyana ainihin adadin fasinjoji da ma’aikatan jirgin da ke cikin jirgin da ya taso daga Bali zuwa Melbourne ba.

A cikin sanarwar da kamfanin ya fitar ta ce “Tsaro da walwalar abokan cinikinmu da ma’aikatan jirgin shi ne babban abin fifikonmu kuma muna gode musu kan yadda suka amsa lamarin.

“Ba za a taɓa yarda da irin wannan dabi’ar ba, ba za a amince da ita ba a cikin jirginmu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza: Isra’ila ta kashe Falasdinawa 58 a awa 58
  • Gaza: Isra’ila ta kashe Falasindawa 58 a awa 58
  • Tsofaffin Ma’aikatan FRCN Za Su Gudanar da Zanga-zanga Kan Jinkirin Biyan Hakkokin Su
  • Kasar Sin Ta Nanata Kudurinta Na Ci Gaba Da Bude Kofa Yayin Wani Taro Da Kamfanonin Amurka 
  • Kasashen Mali da Nijar da Burkina Faso sun kira jakadunsu daga Aljeriya
  • ACF Ta Bukaci Gwamnatin Najeriya Da Ta Kawo Karshe Tashe-Tashen Hankula Filato
  • Kicibus: An Gabza Yaki Tsakanin Yan Bijilanti Da ‘Yan Fashi, Sun Kashe Barayi 30 A Zamfara
  • Fasinja ya yi ƙoƙarin buɗe ƙofar jirgi a sararin samaniya
  • Ana Ci Gaba Da Kai Ruwa Rana Takanin Amurka Da China Kan Batun Harajin Fito
  • Finafinan Kannywood da suke tashe da kuma manyan marubutansu