HausaTv:
2025-03-09@20:12:34 GMT

Jamus, Faransa, Birtaniya Da Italiya Sun Yi Maraba Da Shirin Larabawa Kan Gaza

Published: 9th, March 2025 GMT

Kasashen Jamus, Faransa, Birtaniya da Italiya “sun yi maraba” da shirin kasashen Larabawa na sake gina Gaza.

 A cikin wata sanarwa ta hadin guiwa da ministocin harkokin wajen kasashen suka fitar a birnin Berlin, sun ce shirin idan an aiwatar da shi zai bada damar gaggauta warware mummunan halin da Falasdinawa ke ciki a Gaza.

A yayin taron da suka gudanar ne a ranar Talata data gabata a Masar kasashen Larabawan suka gabatar da wani shiri da zai lakume dalar Amurka Biliyan 53 na sake gina Gaza cikin fiye da shekara biyar inda shirin zai mayar da hankali kan taimakon gaggawa,dawo da ababen more rayuwa da kuma ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

Shirin na kasashen Larabawa tamakar neman maye gurbin shirin da shugaban Amurka Donald Trump, ya fitar a watan da ya gabatar na karbe iko da zirin Gaza dama tilasta musu hijira zuwa kasashen Masar da Jordan.

Matakin na Trump dai ya fuskanci martini da tofin Allah tsine daga daga Falasdinawa da kasashen Larabawa da kuma gwamnatoci da yawa a duniya, inda sukayi fatali da duk wani shiri na korar mutanen Gaza daga kasarsu ta asali.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasashen Larabawa

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Birtaniya Na Cewa Tehran Na Barazana Ga Tsaron Kasar

Jamhuriyar Musulinci ta Iran ta yi watsi da zarge-zargen da jami’an Birtaniya suka yi na cewa Tehran na barazana ga tsaron kasar ta Burtaniya.

A cewar jami’an Iran, Ingila na zargin Iran da wani abu da ta yi fice a kai.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghai, ya mayar da martani da kakkausan lafazi kan wannan zargi, yana mai cewa wannan maganar banza ce.

A cikin wani sako da ya wallafa a shafin X, ya tunatar da cewa ita kanta kasar Birtaniya kwarariya ce wajen tsoma baki cikin harkokin cikin gidan wasu kasashe.

A kwanakin baya ne sakataren tsaron Burtaniya Dan Jarvis ya gabatar da shawarar a gaban majalisar dokokin kasar cewa za a kara sa ido kan gwamnatin Iran da suka hada da jami’an tsaronta da kuma dakarun kare juyin juya halin Musulunci a karkashin wani sabon tsari don dakile barazanar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhin Bayan Labarai: Kasashen Afirka Sun Kori Sojojin Faransa Daga Kasashensu
  • Shugabannin Larabawa Sun Amince Da Tsarin Gina Gaza Da Zai Lakume Dala Biliyan 53
  • Kasashen Turai sun goyi bayan shirin Larabawa na sake gina Gaza
  • Qatar Ta Ce Bata Goyon Bayan Yakin Don Warware Shirin Nukliyar Kasar Iran
  • Aragchi: Hare-hare Kan Cibiyoyin Makamashin Nukliya Na Kasar Iran Ba Za Su Wargaza Shirin Ba
  • OIC Ta Yi Maraba Da Shirin Gwamnatocin Larabawa Na Sake Gina Zirin Gaza
  • Majalisar wakilai na shirin ƙwace rajistar jam’iyyu daga hannun INEC
  • Yansanda A Najeriya Sun Kama Yan Kasar Pakistan Biyu Da Hakanni Wajen Sake Yan Kasashen Waje A Kasar
  • Iran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Birtaniya Na Cewa Tehran Na Barazana Ga Tsaron Kasar