Daga karshe Abubakar Waziri Bado ya yi kira da a maimakon malamai su koma gefe su na zagi yan fim kamata ya yi ace su shigo cikin harkar a dama dasu, domin kuwa yanzu wani lokaci ne da ake ciki inda da dama mutane sun fi kallon fina-finai fiye da yadda su ke kallon karatuttukan malaman addini, saboda haka su shigo a hada karfi da karfe wajen kara tsaftace wannan masana’antar don kuwa ni ma kaina da ace ba jarumin fim bane ni , to da tabbas zan zama malamin addinin musulunci saboda ina matukar sha’awar ganin al’umma ta gyaru.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Jarumi Kannywood

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Mali da Nijar da Burkina Faso sun kira jakadunsu daga Aljeriya

Kasashen Mali, Nijar da kuma Burkina faso dake hade a kawancen Sahel na AES, sun sanar da kiran jakadunsu a Aljeriya domin tuntuba.

A wata sanarwa da aka karanta a gidan talabijin na kasar Mali a yammacin jiya Lahadi, kasashen uku sun sanar da kirawo jakadunsu domin tuntuba bayan da Aljeriya ta kakkabo wani jirgi marar matuki na kasar Mali a farkon wannan wata.

Aljeriya dai ta kakkabo jirgin sojojin na Mali marar matuki a cikin daren ranar 31 ga Maris zuwa 1 ga Afrilu, matakin da kasashen uku sukayi tir da shi.

A cewar gwamnatin Algiers, jirgin mara matuki da ake magana a kai ya shiga cikin kasar ne, saidai sojojin Mali sun tabbatar da cewa jirgin bai shiga cikin kasar Aljeriya ba.

Lamarin, wanda ya faru mako guda da ya gabata, kaashen na AES a wata sanarwa ta bai daya sun bayyana shi a matsayin “rashin gaskiya” da kuma keta dokokin kasa da kasa.

Firaministan Mali Abdoulaye Maiga ya musanta ikirarin Aljeriya na cewa jirgin mara matuki ya shiga sararin samaniyar Aljeriya, yana mai cewa lamarin ya nuna yadda Aljeriya ke goyon bayan ta’addanci.

A matsayin mayar da martani, Mali ta gayyaci jakadan Aljeriya tare da yanke shawarar janyewa daga kawancen sojan yankin na tsawon shekaru goma sha biyar.

Bidiyon da kungiyoyin ‘yan tawaye suka fitar ya nuna tarkacen jirgin da kamfanin Baykar na Turkiyya ya kera.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Garin Neman Gira Amurka Za Ta Rasa Ido
  • Sojoji 2 Da ’Yan Ta’adda Da Dama Sun Rasu A Wani Gumurzu A Borno
  • Ya Kamata Lambar Yabo Ta Zama Hanyar Ƙarfafa Mana Gwuiwa – Misis Nda-Isaiah
  • Kasar Sin Ta Nanata Kudurinta Na Ci Gaba Da Bude Kofa Yayin Wani Taro Da Kamfanonin Amurka 
  •  Kasashen Iran, Rasha Da China Za Su Yi Taro A Moscow Domin Tattauna Batutuwa Da Dama
  • Kasashen Mali da Nijar da Burkina Faso sun kira jakadunsu daga Aljeriya
  • Sojoji biyu da gomman ’yan ta’adda sun rasu a artabu a Borno
  • An sake kona Kur’ani mai tsarki a kasar Netherlands
  • Kanwan Katsina Ya Yabi Gwamnatin Katsina Kan Farfado Da Al’adar Hawan Durbar
  • An yi wa wata mata ƙarin jini sau 36