HausaTv:
2025-04-09@00:31:32 GMT

WHO Za Ta Bai Wa Najeriya Magungunan Cutar Kuturta

Published: 9th, March 2025 GMT

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce za ta aika da magungunan cutar kuturta zuwa Najeriya.

Wannan dai na zuwa ne bayan jinkirin da aka samu na gwaje-gwajen da hukumar ke gudanarwa, lamarin da ya jawo dubban masu fama da cutar ciki har da yara ba su samu magungunan da suka kamata na kare cutar ba.

Kakakin hukumar ta WHO ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters cewar, an samu ƙarancin maganin cutar ta kuturta a Nijeriya.

Ya ce hukumar ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta miƙa buƙatar ganin an samu izinin shigar da maganin cikin ƙasar akan lokaci, kuma a watan Janairu aka amince da hakan.

Nijeriya wadda ita ce ƙasar Afirka da ta fi yawan jama’a na bayar da rahoton samun aƙalla mutum 1,000 da cutar kuturta a duk shekara, wadda cuta ce da ke kama fatar jiki da jijiyoyi da idanu.

Ana iya magance cutar bayan shan magani na wani lokaci, amma idan ba a shan magani, cutar na ƙaruwa, idan take jawo gyambo da kuma nakasa kamar makanta da shanyewar rabin jiki.

Haka kuma, masu fama da cutar na fuskantar hantara da tsangwama a cikin al’umma.

Sai dai magungunan da Nijeriya take da su na cutar sun ƙare a farkon shekarar 2024 sakamakon jinkirin da aka samu na sabbin dokokin cikin gida da aka samar na gwaje-gwaje kan magungunan da ake shigar da su cikin ƙasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Ci Gaba Da Gudanar Da Taron Bita Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ci gaba da gudanar da  tarurrukan bita ga maniyyata aikin Hajjin bana, bayan  kammala azumin watan Ramadan.

Daraktan Hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga Rediyon Najeriya a Dutse, babban birnin jihar.

A cewarsa, hukumar za ta tabbatar da cewa maniyyata sun sami horo da ilimi kan yadda ake aiwatar da aikin Hajji domin dacewa wannan ibada da suka kashe makudan kudade don gannin sun aiwatar da ita.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce, za a wayar da kan alhazai da kuma koya musu yadda za su kula da kansu da kuma yadda za su aiwatar da aikin Hajji bisa ga koyarwar addini.

Ya ce, ana gudanar da wannan taron bitar ne a kullum, a cibiyoyi 27 da aka ware a fadin jihar.

Haka kuma, ya ce, taron bitar zai  taimakawa Alhazan wajen fahimtar dokoki da sabbin tsare-tsaren da hukumomin Saudiyya da hukumar Hajji ta kasa NAHCON suka tsara domin aikin Hajjin shekarar 2025.

Labbo ya yi kira ga dukkanin alhazan bana da su rika halartar wadannan tarurruka domin sanin abubuwan da suka dace.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma yaba maniyyatan bisa yadda suke daukar wannan taron koyarwa da muhimmanci.

Daraktan ya kuma shawarce su da su ci gaba da nuna dabi’un kirki kamar yadda suka saba, tare da zama jakadu nagari ga jihar, da kasa baki daya, tare da bin doka da oda a masarautar Saudiyya.

Ya ce, hukumar ta riga ta tanadi masauki mai tsafta kusa da Masallacin Harami ga alhazan jihar, tare da shirya yadda za a rika ba su abinci ta hannun wani kamfani na kasar Saudiyya.

Labbo ya kuma yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da hadin kai da yake bai wa hukumar a kowane lokaci.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Ci Gaba Da Gudanar Da Taron Bita Ga Alhazai
  • Najeriya: An gudanar da zanga-zangar adawa da wasu shirye-shiryen  gwamnati
  • An Buɗe Sabbin Cibiyoyin Kula Da Masu Cutar Sankarau A Jihohi 6
  • Saudiyya ta sanya wa masu Umarah wa’adin ficewa daga ƙasar
  • HOTUNA: Yadda zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu ta gudana a wasu biranen Nijeriya
  • HOTUNA: Zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu ta ɓarke a Abuja da Legas
  • Mutanen da Sanƙarau ta kashe sun kai 151 — NCDC
  • Zanga-zangar da za mu yi babu gudu babu ja da baya — Take It Back
  • Arzikin Nijeriya Ya Habaka Zuwa Naira Tiriliyan 22.61 A Zangon Karshe Na 2024 – CBN
  • An yi wa wata mata ƙarin jini sau 36