Gwamnatin Sahayoniya ta hana Falasdinawa masu ibada yin I’itikafi a Masallacin Al-Aqsa
Published: 9th, March 2025 GMT
A yammacin ranar Alhamis da ta gabata ce sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila suka aukawa Falasdinawa masu ibada bayan sun gudanar da sallar tarawihi a masallacin Al-aqsa, inda suka kore su daga masallacin da karfi, tare da hana su yin I’itikafi a cikin masallacin.
Da yake tsokaci a cibiyar yada labaran Falasdinu, Ziad Abhais, mai bincike kan al’amuran birnin Kudus, ya jaddada cewa, matakin da gwamnatin sahyoniyawa ta dauka na hana masu ibadar I’itikafi a cikin masallacin Al-Aqsa wani mataki ne na cin zarafi da kuma muzgunawa hakkokinsu na addini.
Ya kara da cewa: Sojojin yahudawan sahyoniya suna amfani da hakan ne don shimfida ikonsu a kan masallacin Al-Aqsa, domin kuwa a shekara ta 2015 an ba da izinin yin I’itikafi a cikin wannan masallaci a duk ranakun watan Ramadan.
Hukumar bayar da agaji ta Musulunci a birnin Kudus ta sanar da cewa sama da masu ibada dubu 80 ne suka gudanar da sallar isha’i da tarawihi a harabar masallacin Al-Aqsa mai albarka a yammacin ranar Alhamis, wadanda akasarinsu mazauna birnin Kudus ne da yankunan da yahudawa suka mamaye a shekara ta 1948.
A daidai lokacin da watan Ramadan ya shiga, sojojin Isra’ila sun jibge dakaru masu yawa a birnin Kudus da kuma kewayen masallacin Al-Aqsa don hana Falasdinawa masu ibada shiga masallacin .
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Fararen hula 162 sun rasa rayukansu a tashe-tashen hankulan a lardunan gabar tekun Syria
Rahotanni da ke fitowa daga kasar suna nuni da cewa, Yawancin fararen hula da aka kashe a tashe-tashen hankulan da suka faru a wannan Juma’a, dakarun sabuwar gwamnatin kasar ta Syria ne suka kashe su, kamar yadda binciken kungiyar kare hakkin bil Adam ta (SOHR) ya tabbatar.
Ayyukan tashe-tashen hankulan sun yi sanadin Kisan mutuwar fararen hula 162 a lardunan gabar tekun Syria, ciki har da mata da kananan yara, in ji rahoton kungiyar ta SOHR.
Akasarin wadanda aka kashe dai kamar yadda aka gani a wasu fayafayin bidiyo da aka dauka, jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria ne da suke da alaka kungiyoyi masu tsatsauran ra’ayi irin su Tahrir Sham da makamantansu da suke da alaka da Alqaida ne suka kama mutanen, bisa tuhumar cewa suna da alaka da tsohuwar gwamnatin Bashar Assad, a kan haka suka yanke musu hukuncin kisa a nan take kuma suka kashe su.
Kungiyar ta ce wannan matakin na nuni da irin mawuyacin hali mai matukar hadari da Syria ta fada a ciki, inda ake ci gaba da cin zarafi jama’a da kuma muzguna musu da sunan daukar fansa a kan tsiraru marasa rinjaye.
Wasu daga cikin Hotunan da aka dauka sun yadu a shafukan sada zumunta, wadanda suke nuni da manyan laifukan yaki. Rahoton ya ce wasu daga cikin faifan bidiyo sun nuna lokacin da jami’an tsaron sabuwar suka harbe wasu ‘yan kasar Syria da ba su dauke da makami, wadanda aka wulakanta su kafin a yi musu kisan gilla.