HausaTv:
2025-04-29@08:08:26 GMT

Kasashen Turai sun goyi bayan shirin Larabawa na sake gina Gaza

Published: 9th, March 2025 GMT

Manyan kasashen Turai, da suka hada da Burtaniya, Faransa, Jamus, da Italiya, sun goyi bayan shawarar Masar na sake gina Gaza a matsayin mai adawa da shirin “riviera” na shugaban Amurka Donald Trump wanda ke ba da shawarar korar Falasdinawa da karfi daga yankin.

Duk da goyon bayansu da kuma wanke ayyukan kisan kare dangi da Isra’ila ke yi a zirin Gaza tun farkon yakin a watan Oktoban 2023, ministocin harkokin wajen Birtaniya, Faransa, Jamus, da Italiya sun sanar a cikin wata sanarwa a ranar Asabar cewa sun amince da shirin Masar wanda zai inganta “mummunan yanayin rayuwa da Falasdinawa suke ciki a Gaza.

Sanarwar ta kara da cewa, “Shirin ya nuna wata hanya ta sake gina Gaza idan aka aiwatar da hakan cikin gaggawa.

A ranar Asabar ne kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC mai mambobi 57 ta amince da shawarar kungiyar hadin kan kasashen Larabawa a hukumance kan sake gina Gaza a wani taron gaggawa da ta gudanar a kasar Saudiyya.

OIC ta bukaci “kasashen duniya da cibiyoyin bayar da kudade na kasa da kasa da na shiyya-shiyya da su gaggauta ba da tallafin da ya dace ga shirin.”

Wani cikakken daftarin shirin sake gina Gaza da Masar ta gabatar ya hada da ware dala biliyan 53 don sake gina gina yankin, da kuma batun kafa kwamitin gudanarwa domin tafiyar da yankin zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Rasha Ta Fara Aika Isakar Gas Zuwa Kasar  Iran Ta Azarbaijan Don Sayarwa A Kasuwannin Duniya

Kasar Rasha ta fara tura iskar gasa zuwa kasar Iran ta kasar Azarbaijan, wanda daga karshe zai shiga kasuwan ga kasar ta rasah.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto gwamnatin kasar ta na fadar haka a yau Asabar.

Labarin ya kara da cewa tun taron kwamin hadin guiwa na kasuwanci da tattalin arziki na kasashen biyu ya gudanar da taronsa na hadin guiwa karo na 18 a birnin Mosco, Rasha ta bada sanarwan fara tura iskar gas zuwa kasar ta Iran ta kasar Azirbajan, wanda kuma hakan zai zama kasuwa ga kasar Rasha amma a kasar Iran..

Kasashen biyu dai sun dade suna kokarin karfafa dangantaka a tsakaninsu, musamman bayan da kasashen yamma suka dora masu takunkuman  tattalin arziki masu tsananin, saboda yakin da Rasha take yi a Ukraine da kuma saboda shirin Nukliyar kasar Iran ta zaman lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Wajabcin Kawo Karshen Ayyukan Ta’addanci A Kasashen Yanki
  • An Fara Gudanar Da Zaman Taron Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Tsakanin Iran Da Kasashen Nahiyar Afirka
  • Kasashen Duniya Sun Yi Ta AiIka Tallafi Bayan Fashewar Bandar Abbas
  • Iran Ta Bukaci Kasashen Indiya Da Pakistan Da Hada Kai Don Yakar Ta’addanci
  • Wang Yi Ya Ce Kasar Sin Za Ta Magance Cin Zarafin Da Amurka Ke Yi Ita Kadai
  • Bayan Shekaru 10 Madrid Da Barcelona Zasu Sake Yaɗuwa A Wasan Ƙarshe Na Copa Del Rey 
  • Iran Ta Gabatar Da Tayin Shiga Tsakanin Don Sasanta Indiya Da Pakisatan
  • Rasha Ta Fara Aika Isakar Gas Zuwa Kasar  Iran Ta Azarbaijan Don Sayarwa A Kasuwannin Duniya