Mutane 1,018 ne aka kashe a ci gaba da kisan kiyashi kan tsiraru a gabar tekun Syria
Published: 9th, March 2025 GMT
Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama ta Syria ta bayar da rahoton cewa, adadin fararen hula da aka yi kisan kiyashin na baya-bayan nan daga tsiraru ‘yan Alawite ya kai mutane 1,018 tun daga ranar alhamis zuwa wannan Lahadi.
Kungiyar sa ido ta ce jami’an tsaron sabuwar gwamnatin Syria da kuma kungiyoyin da suke kawance da su da suka da alaka da alkaida, sun kashe fararen hula 745 na Alawi a cikin kwanaki uku da suka gabata, wanda ya haura adadin da aka sanar a lokutan baya.
Sai dai Fox News ta buga misali da wata ‘yar Alawiyya, wadda ta bukaci a sakaya sunanta, ta bayyana cewa sama da mutane 4,000 ne aka kiyasta an kashe a yankin gabar tekun Syria da kuma cikin ‘yan Alawiyya.
Kungiyar masu tsatsauran ra’ayin ta Hay’at Tahrir al-Sham wadda ke shugabanci a halin yanzu a Syria, wadda kuma it ace tare da taimakon Turkiya da Amurka da wasu kasashen larabawa ta jagoran jagoranci hare-haren da suka kai ga kawo karshen gwamnatin Assad, ta ce za ta kare tsiraru a kasar, a daidai lokacin da ‘yan bindiga da ke karkashin ikonta a halin yanzu suke yi wa fararen hula yankan rago da sunan cewa suna da alaka da tsohuwar gwamnatin Assad.
Kungiyar sa ido da kare hakkokin dan adam a Syria ta bayar da rahoton ayyukan kisan gilla da dama a cikin ‘yan kwanakin nan, tare da kashe mata da kananan yara.
“Yawancin wadanda aka kashe din an kashe su ne ta hannun wasu da ke da alaka da ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida na sabuwar gwamnatin Syria,” in ji rahoton kungiyar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Nazarin CGTN: Mutane Da Dama A Duniya Sun Yaba Da Salon Shugabancin Gwamnatin Kasar Sin
A bara, alkaluman tattalin arziki na GDP na kasar Sin sun kai yuan triliyan 134.9, inda aka samu karuwar kaso 5 cikin dari, lamarin da ya sa shi kasancewa tattalin arziki mafi saurin ci gaba cikin kasashen duniya masu karfin tattalin arziki. Ci gaban da ake samu na ingantuwar tattalin arzikin kasar ya haifar da tarin alfanu ga jama’a. Wani nazari da ya samu amsa daga mutane 25,883 daga kasashe 41 da kafar yada labarai ta CGTN ta gudanar, ya nuna cewa, sama da kaso 80 na wadanda suka bayar da amsa, sun yaba da tsarin ci gaban kasar Sin dake mayar da hankali kan moriyar al’umma, tare kuma da amincewa da ingancin salon shugabancin gwamnatin kasar Sin.
A shekarar 2024, mizanin aikin yi da na farashin kayayyaki sun kasance kan wani mataki mai daidaito, inda aka samar da guraben ayyukan yi miliyan 12.56 a birane, kana kudin shigar kowanne dan kasa ya karu da kaso 5.1. Baya ga haka, an karfafa tsare-tsaren bayar da ilimin tilas da kula da tsoffi da kiwon lafiya da sauran harkokin al’umma.
Ban Ji Dadin Zaman PSG Ba, Messi Manchester United Na Son Lashe Firimiya A Shekarar 2028Cikin nazarin da CGTN ta gudanar, masu bayar da amsa sun yaba matuka da ingancin shugabancin gwamnatin kasar Sin, inda kaso 78.8 suka ce an cimma gagarumar nasara a harkar bayar da ilimi, kaso 70.1 sun yaba da yadda aka samu karuwar kudin shigar jama’a, kaso 63.4 kuma, sun yaba ne da ingantuwar muhallin rayuwa. Haka kuma, kaso 61 sun yaba da ingantuwar tsarin kiwon lafiya yayin da kaso 58.1 suka yaba da ingantuwar yanayin muhallin halittu. Wasu kaso 62.7 kuma sun ce fa’idojin da manufofin Sin ke da su na da muhimmanci wajen bayar da tabbaci ga ingantaccen tsarin shugabanci a kasar.
An samu wadannan alkaluma ne daga nazarce-nazarce biyu da kafar CGTN da jami’ar Renmin ta kasar Sin suka gudanar ta hannun cibiyar bincike kan harkokin kasa da kasa a sabon zamani, inda suka mayar da hankali kan “Yanayin Zama a Kasar Sin” da “Zamanatar da Kasar Sin”. Masu bayar da amsar sun hada da mutanen yankin arewacin Amurka da nahiyar Turai da Afrika da Oceania da kudu maso gabashin Asiya da gabashi da kudu da tsakiyar Asiya da kuma yankin Gabas ta Tsakiya. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp