Ma’aikatar tsaron kasar Sin ta sanar da fara atisayen sojan ruwa na hadin gwiwa da kasashen Rasha da Iran, wanda za a ci gaba da gudanarwa har zuwa mako mai zuwa a kusa da tashar ruwa ta Chabahar  ta kasar Iran.

Ma’aikatar tsaron kasar Sin ta sanar a yau Lahadi cewa, kasashen Sin, Rasha da Iran sun fara atisayen jiragen ruwa na hadin gwiwa daga tashar ruwan Chabahar ta Iran ne domin karfafa hadin gwiwa na tsaro tsakanin wadannan kasashe guda uku.

Kwanaki biyu da suka gabata, Beijing ta mayar da martani ga kalaman sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth na cewa kasarsa a shirye take domin shiga kowane irin yaki, kuma idan muna son dakile Sinawa ko wasu, dole ne mu kara karfinmu na yaki, inji sakataren tsron na Amurka.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ya ce, kalaman da jami’in na Amurka ya yi suna haifar da sabani da kuma yada abin kasar Sin ke kallonsa a matsayin barazana ga kasarta.

Lin ya kara da cewa, “Muna kira ga Amurka da ta daina gina tunaninta  akan masaniyarta dangane da Sin a lokutan baya, musamman lokacin yakin cacar baki, domin kuwa a yanzu Sin ba wadda Amurka ta san ice a lokutan baya ba.

Sakataren tsaron Amurka ya fada a wata hira da kafar yada labarai ta Fox News a ranar Larabar da ta gabata cewa, Amurka ta shirya tsaf domin shiga kowane irin yaki a duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Na Yaki Da Cin Zalin Da Amurka Ke Yi Ta Hanyar Dora Haraji Ne Bisa Sanin Ya Kamata

Duk da matsin lambar da Amurka ke yi, kasar Sin tana da dabararta, za ta ci gaba da mai da hankali kan ayyukanta, za ta kuma rika bude kofarta ga ketare. Har kullum kasar Sin na ganin cewa, ainihin huldar da ke tsakaninta da Amurka ita ce samun moriyar juna da nasara ga ko wane bangare. Ya kamata a daidaita sabanin ciniki ta hanyar tattaunawa cikin adalci. Amma idan Amurka ta fara dora harajin da ta yi shelar dauka, to, kasar Sin za ta dauki wajibabbun matakai, domin kiyaye halastattun hakkokinta. (Tasallah Yuan)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarayyar Turai Ta Yi Maraba Da Tattaunawa Tsakanin IRAN da Amurka Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya
  • Sojojin Kasar Yamen Sun Maida Martani Ga Hare-Haren Amurka Kan Amurkan Da Kuma HKI
  • Jiragen Yaki Da Sojojin Kasa Na HKI Sun Kashe Falasdinawa 38 A Yankin Gaza Daga Safiyar Yau Zuwa Yanzu
  • Majalisar Jihar Kaduna Ta Bude Bincike Kan Ginin Kasuwa da Aka Yi Watsi da Shi
  • Iran ba ta amince da Amurka ba, amma za ta gwada su (Araghchi)
  • Majalissar Dokokin Rasha ta amince da yerjejeniyar huldar ta shekara 20 da Iran
  • Kasar Sin Na Yaki Da Cin Zalin Da Amurka Ke Yi Ta Hanyar Dora Haraji Ne Bisa Sanin Ya Kamata
  • Jihar Kwara Za Ta Rufe Karbar Kudin Aikin Hajji A Ranar Juma’a
  • Iran da Amurka zasu fara tattaunawa a Oman ranar Asabar
  •  Kasashen Iran, Rasha Da China Za Su Yi Taro A Moscow Domin Tattauna Batutuwa Da Dama