Ma’aikatar tsaron kasar Sin ta sanar da fara atisayen sojan ruwa na hadin gwiwa da kasashen Rasha da Iran, wanda za a ci gaba da gudanarwa har zuwa mako mai zuwa a kusa da tashar ruwa ta Chabahar  ta kasar Iran.

Ma’aikatar tsaron kasar Sin ta sanar a yau Lahadi cewa, kasashen Sin, Rasha da Iran sun fara atisayen jiragen ruwa na hadin gwiwa daga tashar ruwan Chabahar ta Iran ne domin karfafa hadin gwiwa na tsaro tsakanin wadannan kasashe guda uku.

Kwanaki biyu da suka gabata, Beijing ta mayar da martani ga kalaman sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth na cewa kasarsa a shirye take domin shiga kowane irin yaki, kuma idan muna son dakile Sinawa ko wasu, dole ne mu kara karfinmu na yaki, inji sakataren tsron na Amurka.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ya ce, kalaman da jami’in na Amurka ya yi suna haifar da sabani da kuma yada abin kasar Sin ke kallonsa a matsayin barazana ga kasarta.

Lin ya kara da cewa, “Muna kira ga Amurka da ta daina gina tunaninta  akan masaniyarta dangane da Sin a lokutan baya, musamman lokacin yakin cacar baki, domin kuwa a yanzu Sin ba wadda Amurka ta san ice a lokutan baya ba.

Sakataren tsaron Amurka ya fada a wata hira da kafar yada labarai ta Fox News a ranar Larabar da ta gabata cewa, Amurka ta shirya tsaf domin shiga kowane irin yaki a duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Da Iraki Sun Nuna Damuwa Kan Tashe-tahen Hankula A Siriya

Kasashen Iran da kuma Iraki sun nuna damuwa kan tashe tashen hankulan dake faruwa a Siriya.

A wata sanarwa da ta fita ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta bayyana matukar damuwarta kan yadda tashe-tashen hankulan da ke yaduwa a fadin kasar ta Siriya, tana mai gargadin cewa, wannan yanayi mara kyau zai share fagen rashin zaman lafiya a yankin da kuma kara tunzura Isra’ila.

Kakakin ma’aikatar Esmail Baghai ya bayyana cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran na nuna damuwa kan rashin tsaro, tashe-tashen hankula, zubar da jini da cutar da al’ummar Siriya da basu ji basu gani ba.

Ita ma ma’aikatar harkokin wajen kasar Iraki ta bayyana matukar damuwarta kan halin da ake ciki a makwabciyarta Syria, tana mai jaddada cewa karuwar tashe-tashen hankula a kasar Larabawar ka iya yin tasiri sosai ga tsaro da zaman lafiyar yankin.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a Asabar din nan, ma’aikatar ta jaddada bukatar “kare fararen hula daga bala’in rikici.”tare da yin kira da a ba da fifiko wajen tattauna hanyoyin warware matsalar ta cikin lumana.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da wasu majiyoyi na cikin gida suka bayar da rahoton cewa, an gwabza kazamin fada tsakanin bangarorin da ke da alaka da gwamnatin Hayat Tahrir al-Sham (HTC) mai mulki da kuma ‘yan adawa masu biyayya ga tsohuwar gwamnatin, kusa da asibitin al-Watani da ke birnin As-Suwayda a kudu maso yammacin kasar Syria.

Kungiyar kare hakkin dan adam ta Syrian Observatory for Human Rights (SOHR) mai hedkwata a birnin Landan ta bayar da rahoto a jiya Juma’a cewa akalla mutane 237 ne aka kashe a yankin gabar tekun Syria tun bayan barkewar sabon tashin hankali a ranar Alhamis.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Gobe Litinin Za A Yi Atisayen Sojan Ruwa Na Hadin Gwiwa Tsakanin Kasashen Iran, Rasha Da China
  • Oficin Jakadan Iran A MDD Ya Ce Babu Wani Sako Da Suka Karba Daga Shugaban Kasar Amurka
  • Iran Da Iraki Sun Nuna Damuwa Kan Tashe-tahen Hankula A Siriya
  • China Ta Yi Gargadin Cewa Duniyar Zata Zama Ba Doka Da Oda Idan Amurka Ta Ci Gaba Da Yakin Kudaden Fito Da Ta fara
  • An Kashe Mutum Akalla 70 A Yaki Tsakanin HKS Da Yan Tawaye A Kudancin Kasar Siriya
  • Kasar Chaina Ta Yi Gargadin Cewa Duniyar Zata Zama Ba Doka Da Oda Idan Amurka Ta Ci Gaba Da Yakin Kudaden Fito Da Ta fara
  • Araghchi Ya Tafi Saudiyya Domin Halartar Taron OIC
  • Iran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Birtaniya Na Cewa Tehran Na Barazana Ga Tsaron Kasar
  • Nijeriya Za Ta Fara Aiwatar Da Yarjejeniyoyin Haɗin Gwiwa Da Kafofin Watsa Labarai Na Sin – Ministan Yaɗa Labarai