Kamfanin dillancin labarun “ Irna” ya nakalto cewa; Jiragen ruwa na soja da kuma dakarun kare juyin musuluni na Iran za su shiga cikin atisayen na hadin gwiwa da kasashen Rasha da kuma China.

Bugu da kari da akwai wasu kasashen da za su turo sojojin masu sa ido, da su ne; jamhuriyar Azerbaijan, Afirka Ta Kudu, Oman, Khazakistan da Pakistan.

Sai kuma kasashen Katar, Iraki, HDL da kuma Srilanka.

Wannan atisayen dai za a yi ne a sansani na uku na sojan ruwan Iran wanda yake a arewacin tekun Indiya.

Manufar wannan atisayen dai shi ne  bunkasa yadda kasashen za su rika aiki tare a tsakanin kasashen sojojin ruwan Iran, Rasha da kuma China.

Wannan dai ba shi ne karon farko da sojojin ruwan kasashen Iran Rasha da kuma China su ka yi atisayen soja na hadin gwiwa ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kudaden Musanyar Kasashen Waje Da Sin Ta Adana Sun Kai Fiye Da Dala Tiriliyan 3.2 A Watanni 16 A Jere

Alkaluman da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta samar sun shaida cewa, ya zuwa karshen watan Maris na bana, yawan kudaden musanyar kasashen waje da Sin ta adana ya kai dala tiriliyan 3.2407, adadin da ya karu da kashi 0.42%, wato da dala biliyan 13.4 bisa na makamancin watan Fabrairu. Hakan ya sa yawan kudaden ya kai fiye da dala triliyan 3.2 a cikin watanni 16 a jere.

 

An kuma bayyana cewa, a watan da ya gabata, tattalin arzikin Sin ya ci gaba da tafiya yadda ya kamata ba tare da tangarda ba, inda jerin manufofin da aka bullo da su bisa yanayin da ake ciki da wadanda za a dauka bisa sauye-sauyen da ake fuskanta, na ci gaba da nuna tasirinsu a kan yakini, kuma duba da ingantacciyar bunkasar da ake samu, matakan suna kara tabbatar da yawan kudaden musanyar kasashen waje da Sin ta adana a cikin yanayi mai dorewa. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Inganta Aminci Da Hadin Gwiwa A Asiya
  • Pezeshkian: Dole ne Amurka ta tabbatar da cewa da gaske take yi a game da tattaunawa
  • Dangantaka ta yi tsami tsakanin Aljeriya da kasashen kawancen Sahel
  • Kudaden Musanyar Kasashen Waje Da Sin Ta Adana Sun Kai Fiye Da Dala Tiriliyan 3.2 A Watanni 16 A Jere
  •  Kasashen Faransa Masar Da Jordan Sun Yi Taro Akan Gaza
  • Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 30 a Kongo
  •  Kasashen Iran, Rasha Da China Za Su Yi Taro A Moscow Domin Tattauna Batutuwa Da Dama
  • Cin Zali Ba Zai Iya Hana Kasashen Afirka Ci Gaba Ba
  • Iran : kasashen turai sun tafka kure na tarihi, ta hanyar goyan bayan Isra’ila
  • Ana Ci Gaba Da Kai Ruwa Rana Takanin Amurka Da China Kan Batun Harajin Fito