HausaTv:
2025-04-10@05:35:12 GMT

Kalibaf: Maganar Donald Trump Akan Tattaunawa Da Iran Yaudara Ce

Published: 9th, March 2025 GMT

Shugaban Majalisar shawarar musulunci ta Iran Muhammad Bakir Kalibaf, ya bayyana cewa; Babu yadda za a yi Iran ta zauna teburin tattaunawa da gwamnatin Amurka alhali tana yi ma ta barazana.

Har ila yau ya ce zancen bayan nan na shugaban kasar Amurkan akan tattaunawa manufarsa ita ce yaudara da kuma kokarin raba Iran da karfinta.

A yau Lahadi ne shugaban majalisar shawarar musuluncin ta Iran ya bayyana haka, yana mai kara da cewa; Kasarsa ba ta jiran wani sako  daga Amurka, kuma za ta dakile dukkanin takunkuman da ta kakaba mata ta hanyar dogaro da karfin tattalin arzikinta da kuma alakarta ta kasa da kasa.

Shugaban majalisar shawarar musuluncin ta Iran ya kuma ce; Yadda Donald Trump ya yi mu’amala da sauran kasashe, yana tabbatar da cewa managarsa akan tattaunawa yaudara ce, da kuma son raba Iran da karfin da take da shi, ta hanyar sanya ta ja da baya akan wasu tsare-tsarenta na tsaro.

 A cikin kwanakin nan ne dai Donald Trump ya yi batun aikewa da Iran sako yana kiranta zuwa tattaunawa, lamarin da Tehran ta kore.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 HKI Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Yankin Khan-Yunus

A rana ta 21 da Isra’ila ta sake komawa yaki da al’ummar Falasdinu a Gaza, jiragen yakinta sun kai hare-hare munanan a yankin Khan-Yunus da ya yi sanadiyyar shahadar mutane da dama, da kuma jikkata wani adadin Falaasidinawa  mai yawa.

Jim kadan bayan kai wannan harin ne dai kungiyar  ta mayar da martini ta hanyar harba makamai masu linzami akan matsugunin ‘yan share wuri zauna a Asqalan da hakan ya yi sanadiyyar jikkatar ‘yan sahayoniya.

A gafe daya ana gudanar da yajin aiki na gama gari a yankin yammacin kogin Jordan saboda nuna kin amincewa da yadda ‘yan sahayoniya suke yi wa al’ummar Falasdinu kisan kiyashi. Kungiyoyin fararen hula ne su kirayi wannan yajin aikin, wanda ya game yankin na yammacin kogin Jordan.

A wani labarin daga Gaza, ma’aikatar kiwon lafiya ta sanar da cewa da akwai mutanen da sun  haura miliyan biyu da suke fama da matsalar rashin abinci mai gina jiki.

Ma’aikatar ta yi wannan sanarwar ne adaidai lokacin da ake raya ranar lafiya ta duniya, tana mai kara da cewa; a kowane lokaci yanayin kiwon lafiya a zirin Gaza yana kara tabarbarewa.” Haka nan kuma ta yi gargadi akan rufe dukkanin hanyoyin shigar da abinci cikin yankin da hakan yake jefa rayuwar yara masu yawan gaske cikin hatsari.

Wani batu da hukumar kiwon lafiya ta yankin na Gaza, ta yi gargadi a kansa, shi ne yadda Isra’ila ta hana a shigar da riga-kafin shan inna cikin yakin, da hakan zai rusa kokarin da aka yin a watanni 7 a baya na fada da wannan cuta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce Iran Ba Zata Jada Bayan Ba A Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya
  • Tarayyar Turai Ta Yi Maraba Da Tattaunawa Tsakanin IRAN da Amurka Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya
  • Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Barcelona Da Borrusia Dortmund 
  • Iran: Tattaunawa kai tsaye da Amurka a yanzu ba shi ne zabinmu ba
  • Pezeshkian: Dole ne Amurka ta tabbatar da cewa da gaske take yi a game da tattaunawa
  • Iran da Amurka zasu fara tattaunawa a Oman ranar Asabar
  •  Kasashen Faransa Masar Da Jordan Sun Yi Taro Akan Gaza
  •  HKI Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Yankin Khan-Yunus
  • Arakci: Amruka Tana Mafarkin Kulla Yarjejeniya Da Iran Kwatankwanci Wacce Ta Yi Da Kasar Libya
  • Araqchi: Babu Wata Tattaunawa Da Aka Gudanar Tsakanin Amurka Da Iran