HausaTv:
2025-03-10@01:23:18 GMT

Kalibaf: Maganar Donald Trump Akan Tattaunawa Da Iran Yaudara Ce

Published: 9th, March 2025 GMT

Shugaban Majalisar shawarar musulunci ta Iran Muhammad Bakir Kalibaf, ya bayyana cewa; Babu yadda za a yi Iran ta zauna teburin tattaunawa da gwamnatin Amurka alhali tana yi ma ta barazana.

Har ila yau ya ce zancen bayan nan na shugaban kasar Amurkan akan tattaunawa manufarsa ita ce yaudara da kuma kokarin raba Iran da karfinta.

A yau Lahadi ne shugaban majalisar shawarar musuluncin ta Iran ya bayyana haka, yana mai kara da cewa; Kasarsa ba ta jiran wani sako  daga Amurka, kuma za ta dakile dukkanin takunkuman da ta kakaba mata ta hanyar dogaro da karfin tattalin arzikinta da kuma alakarta ta kasa da kasa.

Shugaban majalisar shawarar musuluncin ta Iran ya kuma ce; Yadda Donald Trump ya yi mu’amala da sauran kasashe, yana tabbatar da cewa managarsa akan tattaunawa yaudara ce, da kuma son raba Iran da karfin da take da shi, ta hanyar sanya ta ja da baya akan wasu tsare-tsarenta na tsaro.

 A cikin kwanakin nan ne dai Donald Trump ya yi batun aikewa da Iran sako yana kiranta zuwa tattaunawa, lamarin da Tehran ta kore.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Al-Houthi: Mun Baiwa Isra’ila Wa’adin Kwanaki 4 Da Ta Kawo Karshen Killace Gaza

Jagoran kungiyar Ansar Allah ta kasar Yemen, Sayyed Abdul-Malik al-Houthi, ya baiwa masu shiga tsakani wa’adin kwanaki hudu na tabbatar da shigar da kayayyakin jin kai a Gaza, yana mai gargadin cewa idan har Isra’ila ta ci gaba da toshe hanyoyin kai kayan agaji a Gaza, to dakarun Yemen za su ci gaba da kai hare-hare kan jiragen ruwa masu alaka da Isra’ila.

A cikin wani jawabi da ya yi wanda aka watsa a gidajen talabijin na ciki da wajen kasar Yemen, Al-Houthi ya soki ta’annutin da  Isra’ila ke ci gaba da yi wa Falasdinu, yana mai jaddada cewa, rashin aiwatar da yarjejeniyar dakatar da bude wuta da kuma hana shigar da kayan agaji a Gaza da kuma ci gaba da killace yankin da Haramtacciyar Kasar Isra’ila ke yi, lamari ne mai matukar hadari.

Al-Houthi ya zargi Isra’ila da kin yin aiki da alkawuran da ta dauka a karkashin yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma a kan Gaza, musamman dangane da ayyukan jin kai, yana mai cewa Hamas ta cika dukkanin alkawullanta da kuma sauke nauyin da ya rataya a wuyanta, ta hanyar kiyaye wannan  yarjejeniyar.

Har ila yau Al-Houthi ya yi Allah wadai da zafafa hare-haren da Isra’ila ke kai wa a yankunan yammacin gabar kogin Jordan da kuma al-Quds, yana mai bayyana irin rawar da Isra’ila ke takawa wajen kara kai hare-hare kan Falasdinawa a matsayin laifin yaki.

Baya ga haka kuma, Ya soki yadda Amurka ke goyon bayan mamayar Isra’ila ido rufe a karkashin Shugaba Donald Trump, yana mai cewa goyon bayan Washington ya karfafa gwiwar Isra’ila wajen ci gaba da muzgunawa Falasdinawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DRC Ta Sa Kudi Dalar Amurka Miliyan 5 Akan Jagororin ‘Yan Tawayen M 23
  • Iran : Wadanda Suka Dage Kan Tattaunawa Da Iran, Na Yi Ne Don Amfanin Kansu_ Jagora
  • Jagora: Iran, Tabbas Zata Ki Amincewa Da Tattaunawa Da Kasashe Masu Girman Kai
  • Oficin Jakadan Iran A MDD Ya Ce Babu Wani Sako Da Suka Karba Daga Shugaban Kasar Amurka
  • Al-Houthi: Mun Baiwa Isra’ila Wa’adin Kwanaki 4 Da Ta Kawo Karshen Killace Gaza
  •  Ayatullah Khatami: Tattaunawa Da Amurka Kaskanci  Ne
  • Damuwar IMF akan kalubalen tattalin arzikin Najeriya yaudara ne – Farfesa Yushau Ango
  • An Bukaci ‘Yan Su Matsa Kaimi Har Sai Anbiya su Hakokinsu
  • Hamas Ta Ce A Shirye Take Kan Komi, Kan Barazanar Trump