Wani mutum wanda yake nuna kin amincewa da zaluncin da HKI yake yi wa mutanen Gaza, ya hau kan hausumiyar agogon “ Big-Bang”   a birnin London dauke da tutar Falasdinu.

An sami cunkuson motoci a yankin Westminster dake birnin London a jiya Asabar,yayin da masu ceto suke kokarin isa ga mutumin domin sauko da shi daga kan hausmiyar agogon.

Jami’an ‘yan sandan sun sanar da samin rahoton abinda ya faru da misalin karfe 7 na safe,kuma sun fara aiki domin ganin an sauko da mutumin cikin lafiya.

Jami’an tsaro sun sanar da cewa an rufe hanyar da take zuwa majalisar saboda abinda ya faru. Haka nan kuma gadar da take zuwa Wesminster  da sauran hanyoyin da suke yankin duk an rufe su.

A kasan hasumiyar wasu mutane sun taru suna bayar da taken nuna goyon baya ga ‘yancin Falasdinu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutum 5 A Yobe

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 10, Sun Kashe Ɗan Bindiga 1 A Katsina
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 10 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Kashe Ɗan Bindiga A Katsina
  • Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Barcelona Da Borrusia Dortmund 
  • Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutum 5 A Yobe
  • Jihar Kwara Za Ta Rufe Karbar Kudin Aikin Hajji A Ranar Juma’a
  • Kisan Isuhu Yellow: ’Yan bindiga sun kai harin ɗaukar fansa
  • Yan Sanda A Saudiya Sun Tsare Wata Bafalasdinya Saboda Bayyana Tutar Kasarta A Kan Jakarta A Masallacin Ka’aba
  • Mali, Nijar, da Burkina Faso sun janye jakadunsu daga Algeria
  • Mahara sun yi garkuwa da fiye da mutum 50 a Katsina
  • Dangantaka ta yi tsami tsakanin Aljeriya da kasashen kawancen Sahel