Wani mutum wanda yake nuna kin amincewa da zaluncin da HKI yake yi wa mutanen Gaza, ya hau kan hausumiyar agogon “ Big-Bang”   a birnin London dauke da tutar Falasdinu.

An sami cunkuson motoci a yankin Westminster dake birnin London a jiya Asabar,yayin da masu ceto suke kokarin isa ga mutumin domin sauko da shi daga kan hausmiyar agogon.

Jami’an ‘yan sandan sun sanar da samin rahoton abinda ya faru da misalin karfe 7 na safe,kuma sun fara aiki domin ganin an sauko da mutumin cikin lafiya.

Jami’an tsaro sun sanar da cewa an rufe hanyar da take zuwa majalisar saboda abinda ya faru. Haka nan kuma gadar da take zuwa Wesminster  da sauran hanyoyin da suke yankin duk an rufe su.

A kasan hasumiyar wasu mutane sun taru suna bayar da taken nuna goyon baya ga ‘yancin Falasdinu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar Tsaro Ta Yi Nasarar Hallaka Wani Jigo Lakurawa A Kebbi

Rundunar hadaka ta jami’an tsaro da suka hada da ‘yan banga sun yi nasarar hallaka  wani kasurgumin jigon kungiyar Lakurawa da aka fi sani da  Maigemu a jihar Kebbi.

Sanarwar da Daraktan Tsaron, Alhaji AbdulRahman Usman Zagga, ya fitar, ta ce an kashe Maigemu ne a ranar Alhamis a Kuncin Baba da ke karamar hukumar Arewa, bayan musayar wuta da jami’an tsoro.

Sanarwar ta ce, wannan nasarar ta zo ne mako guda bayan da Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Nasir Idris ya ziyarci al’ummar Bagiza da Rausa Kade a yankin karamar Hukumar Arewa, domin jajantawa al’ummar yankin bisa kashe wasu mutane shida da ake zargin barayin shanun Lakurawa ne suka yi.

An bayyana cewa, matakin da gwamnan jihar ya dauka kan harkokin tsaro ya haifar da d’a mai ido, domin an yi nasarar kashe jagoran Lakurawan, inda aka aje gawarsa a matsayin shaida a asibitin tunawa da Sir Yahaya.

Sanarwar ta ce , daraktan tsaron ya bukaci mazauna yankin da su ba jami’an tsaro hadin kai, ta hanyar sanar da su bayanan sirri da kuma bayar da rahoton abubuwan da ake zargi a yankunansu, domin tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a jihar.

 

Daga Abdullahi Tukur

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Syria: Kungiyoyi Masu Dauke Da Makamai Suna Ci Gaba Da  Kai Wa Kauyukan Lazikiyya Da Tartus Hare-hare
  • Makahon da ke sana’ar POS
  • Amurka : Trump Ya Katse Tallafin Jami’ar Columbia, Saboda Zanga-zangar Goyon Bayan Falasdinu
  • ‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
  • Rundunar Tsaro Ta Yi Nasarar Hallaka Wani Jigo Lakurawa A Kebbi
  • Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
  • Fashewar tankar mai: Mutum 7 sun mutu, gonaki sun lalace a Neja
  • Wani mutum ya yanke jiki ana salla a Masallaci, ya rasu a asibiti
  • Iran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Birtaniya Na Cewa Tehran Na Barazana Ga Tsaron Kasar