Aminiya:
2025-04-09@10:04:12 GMT

PDP ta sake ɗage babban taronta zuwa Mayun 2025

Published: 9th, March 2025 GMT

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta sake ɗage babban taronta na ƙasa (NEC), zuwa ranar 15 ga watan Mayu, 2025.

A wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar, wanda babban sakatarenta, Sunday Ude-Okoye, ya bayyana hakan.

Iyalan Abacha sun gargaɗi Babangida kan ɓata sunan mahaifinsu An samu tsohon shugaban hukumar tsaron Faransa da zamba

Tun asali, an tsara gudanar da taron ne a ranar 13 ga watan Maris 2025, amma aka ɗage shi saboda wasu zaɓukan cike gurbi da aka gudanar a jihohi daban-daban.

Tun a shekarar da ta gabata ne PDP ta tsara yin wannan babban taro karo na 98, amma ana ci gaba da ɗagewa.

Rahotanni na nuni da cewa matsalolin cikin gida da jam’iyyar ke fuskanta, kamar rikicin shugabanci da rashin daidaiton ra’ayi tsakanin manyan jiga-jiganta, na iya zama dalilin jinkirin.

Yanzu haka, ana sa ran taron zai kasance muhimmin mataki ga makomar jam’iyyar, musamman duba da shirye-shiryenta na fafatawa a babban zaɓen 2027.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babban taro jam iyya Siyasa taro

এছাড়াও পড়ুন:

An sake zanga-zangar kin jinin gwamnatin Netanyahu a Tel-Aviv

A Isra’ila dubban masu zanga-zanga ne suka fito kan titunan birnin Tel Aviv a wata sabuwar zanga-zangar kin jinin gwamnati a daidai lokacin da firaminista Benjamin Netanyahu ya gana da shugaban Amurka Donald Trump a birnin Washington.

Masu zanga-zangar a ranar Litinin sun yi Allah wadai da manufofin Netanyahu, ciki har da yunkurinsa na korar manyan jami’an tsaro da na shari’a na gwamnatin.

Sun kuma yi Allah wadai da sake dawo da yakin kisan kare dangi da ake yi wa al’ummar Gaza.

Iyalan ‘yan Isra’ilar da aka yi garkuwa da su a Gaza su ma sun shiga zanga-zangar, inda suka bukaci a kawo karshen yakin da kuma kulla yarjejeniyar tabbatar da sakin mutanen da aka kama.

Kungiyar dai ta ce za ta saki sauran mutanen da ake garkuwa da su ne kawai idan an sako sauren fursunonin Falasdinawa da Isra’ila ke rike da a gidajen yarinta, da kuma tabbatar da tsagaita bude wuta, da kuma janyewar Isra’ila gaba daya daga Gaza.

A ranar 18 ga watan Maris da ya gabata ne, Isra’ila ta sake kaddamar hari a Gaza wanda ya keta yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma a watan Janairu, inda ta kai hare-haren wuce gona da iri tare da kashe daruruwan Falasdinawa, ciki har da yara sama da 100.

Tun daga wannan lokacin, adadin wadanda suka mutu ya kai 1,391, yayin da wasu 3,434 suka jikkata, a cewar majiyoyin lafiya na Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zulum: Boko Haram na sake kwace iko da wasu yankuna a Borno
  • Saudiyya ta bayar da wa’adin ficewar dukkanin masu aikin Umrah daga kasar
  • Kisan Janar Alƙali: Kotu ta ɗage shari’a zuwa 28 ga Mayu
  • An sake zanga-zangar kin jinin gwamnatin Netanyahu a Tel-Aviv
  • Saudiyya ta sanya wa masu Umarah wa’adin ficewa daga ƙasar
  • Jam’iyyar Labour Ta Yi Barazanar Dakatar Da Peter Obi Da Gwamna Otti
  • JAMB Ta Bankaɗo Jabun Takardun Shaidar Kakammal Sakandire 585 A Shekarar 2025
  • An sake kona Kur’ani mai tsarki a kasar Netherlands
  • Gwamnatin Yobe Ta Ƙaryata Rahoton Bayyanar Boko Haram A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025