Sa’adatu Ali JC ta raba wa mata 150 injinan markaɗe a Gombe
Published: 9th, March 2025 GMT
A yayin bikin Ranar Mata ta Duniya, Hajiya Sa’adatu Ali Isa JC, matar Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Balanga da Billiri, ta tallafa wa mata 150 da injinan markaɗe domin su samu hanyar dogaro da kai.
Da ta ke jawabi yayin rabon kayan, Hajiya Sa’adatu ta ce manufar wannan tallafi ita ce taimaka wa mata su samu sana’a da za ta rage musu dogaro da wasu.
“Wannan tallafi yana da muhimmanci domin zai taimaka wa mata su kula da kansu da iyalansu ba tare da jira komai daga mazajensu ba.
“Wannan kuma wani yunƙuri ne na taimakon jama’a kamar yadda maigidana, Hon. Ali Isa JC, ke yi a kodayaushe,” in ji ta.
Ta bayyana cewa mijinta ya tallafa wa mutum sama da 2,000 da kayan abinci da na noman rani don rage yunwa a cikin al’umma.
Haka kuma, ta taɓa koyawa wasu mata sana’ar yin takalma, wanda har takalmansu ke zuwa ƙasashen waje saboda ingancinsu.
Hajiya Sa’adatu ta ja hankalin matan da suka amfana da injinan da ka da su sayar da su, sai dai su yi amfani da su don amfanin kansu da iyalansu.
“Idan kuka yi amfani da wannan tallafi yadda ya kamata, zai zamo muku wata babbar hanya ta samun riba kamar yadda waɗanda suka koyi sana’ar takalma suka samu nasara,” inji ta.
Sannan ta yi kira ga masu hali da su taimaka wa jama’a, ba sai ‘yan siyasa kaɗai ba, domin hakan zai rage zaman banza da talauci a cikin al’umma.
Wasu daga cikin matan da suka amfana sun jinjina mata, inda suka ce ta zama abin koyi a cikin mata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗan Majalisa Injinan Markaɗe Matar Ali JC Rage Talauci
এছাড়াও পড়ুন:
Zulum: Boko Haram na sake kwace iko da wasu yankuna a Borno
Gwamnan Borno, Babagana Umara Zulum, ya bayyana damuwa kan hare-haren da kungiyar ‘yan ta’addan Boko Haram suke kai wa manyan sojoji a baya-bayan nan.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin da yake jagorantar taron kwamitin tsaro da aka gudanar a zauren majalisar, gidan gwamnati, Maiduguri, yana mai cewa jihar na fuskantar barazanar komawa cikin tashin hankali.
“An gurgunta matsugunan soji da dama musamman a garuruwan Wulgo, Sabongari, Wajirko da sauransu. Alamu na nuna ‘yan ta’adda sun fara nasara akanmu. Don haka wannan abu ne mai matuƙar muhimmanci da muke buƙatar tattaunawa.
“Daga shekaru uku baya zuwa yanzu a hankali zaman lafiya ya fara dawowa Borno, amma lamarin ya sauya a ‘yan kwanakin nan,” in ji shi
Zulum ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta tura jiragen yaƙi masu saukar ungulu, da sabbin jirage marasa matuka da aka saya domin tallafawa ayyukan soja a wuraren da abin ya shafa.
“Duk da muna yaba wa sojojin Najeriya, ‘yan sanda, da jami’an DSS kan kiyaye doka da oda a Borno, dole ne mu kuma faɗi gaskiya, in ba haka ba, duk nasarorin da aka samu ya zuwa yanzu za su tafi a wofi,” a cewarsa
Gwamnan, wanda kuma shi ne Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa maso Gabas, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jajirce waje. Tabbatar da yankin arewa maso gabashin kasar ya samu kulawar da ta kamata.