An yi cikakken zama na uku na taron shekara shekara na majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin da safiyar yau Lahadi a babban dakin taron al’umma dake birnin Beijing, inda zaunannen memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar, wanda kuma shi ne shugaban majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin, Wang Huning ya halarci taron, kana, membobin majalisar guda 14 ne suka gabatar da jawabai.

A jawabinta, mambar majalisar Ge Huijun ta ce, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da wani muhimmin jawabi a wajen babban taron murnar cika shekaru 75 da kafa majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar, jawabin da ya kafa alkabila da samar da babban tushe ga ci gaban harkokin majalisar. Ta ce ya dace membobin majalisar su kara gogewa wajen sauke nauyin aiki, da kara kwarewa a fannonin da suka shafi bada jagoranci ta fuskar siyasa, da bada shawarwari game da ayyukan zamanantar da kasa, da kara tuntuba gami da hidimtawa jama’a, tare kuma da kokarin raya kasa da farfado da al’ummomin kasar. (Murtala Zhang)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Ci Gaba Da Gudanar Da Taron Bita Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ci gaba da gudanar da  tarurrukan bita ga maniyyata aikin Hajjin bana, bayan  kammala azumin watan Ramadan.

Daraktan Hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga Rediyon Najeriya a Dutse, babban birnin jihar.

A cewarsa, hukumar za ta tabbatar da cewa maniyyata sun sami horo da ilimi kan yadda ake aiwatar da aikin Hajji domin dacewa wannan ibada da suka kashe makudan kudade don gannin sun aiwatar da ita.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce, za a wayar da kan alhazai da kuma koya musu yadda za su kula da kansu da kuma yadda za su aiwatar da aikin Hajji bisa ga koyarwar addini.

Ya ce, ana gudanar da wannan taron bitar ne a kullum, a cibiyoyi 27 da aka ware a fadin jihar.

Haka kuma, ya ce, taron bitar zai  taimakawa Alhazan wajen fahimtar dokoki da sabbin tsare-tsaren da hukumomin Saudiyya da hukumar Hajji ta kasa NAHCON suka tsara domin aikin Hajjin shekarar 2025.

Labbo ya yi kira ga dukkanin alhazan bana da su rika halartar wadannan tarurruka domin sanin abubuwan da suka dace.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma yaba maniyyatan bisa yadda suke daukar wannan taron koyarwa da muhimmanci.

Daraktan ya kuma shawarce su da su ci gaba da nuna dabi’un kirki kamar yadda suka saba, tare da zama jakadu nagari ga jihar, da kasa baki daya, tare da bin doka da oda a masarautar Saudiyya.

Ya ce, hukumar ta riga ta tanadi masauki mai tsafta kusa da Masallacin Harami ga alhazan jihar, tare da shirya yadda za a rika ba su abinci ta hannun wani kamfani na kasar Saudiyya.

Labbo ya kuma yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da hadin kai da yake bai wa hukumar a kowane lokaci.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Zamfara Ya Yi Jimamin Rasuwar Ɗan Majalisar Zamfara, Aminu K/Daji
  • Majalisar Jihar Kaduna Ta Bude Bincike Kan Ginin Kasuwa da Aka Yi Watsi da Shi
  • Majalissar Dokokin Rasha ta amince da yerjejeniyar huldar ta shekara 20 da Iran
  • An kori jakadan Isra’ila a Habasha daga taron Tarayyar Afirka
  • Pezeshkian: Dole ne Amurka ta tabbatar da cewa da gaske take yi a game da tattaunawa
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Ci Gaba Da Gudanar Da Taron Bita Ga Alhazai
  • Jam’iyyar Labour Ta Yi Barazanar Dakatar Da Peter Obi Da Gwamna Otti
  •  Kasashen Faransa Masar Da Jordan Sun Yi Taro Akan Gaza
  •  Kasashen Iran, Rasha Da China Za Su Yi Taro A Moscow Domin Tattauna Batutuwa Da Dama
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Rika Bayar Da Maganin Hawan Jini Da Siga Kyauta