HausaTv:
2025-03-10@09:54:33 GMT

Sheikh Qassem: Duk da wahalhalun, Hizbullah tana da karfinta

Published: 10th, March 2025 GMT

Babban sakataren kungiyar Hizbullah Sheikh Naim Qassem ya bayyana cewa, gwagwarmayar al’ummar kasar Lebanon na nan da karfinta, duk da asarorin da ta yi da kuma sadaukarwa.

A wata hira da yayi da tashar talabijin ta Al Manar, Sheikh Qassem ya bayyana cewa, ‘yan gwagwarmaya a kasar Lebanon sun yi nasarar cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta da ta kawo karshen hare-haren da Isra’ila a lokacin da suke kara jajircewa.

Ya jaddada cewa “a koyaushe ana ci gaba da tuntubar juna tsakaninsu da shugaban majalisar Nabih Berri, kuma ba mu yi wata tattaunawa a cikin rauni ba.”

Sheikh Qassem ya tabbatar da cewa, muddin Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta ci gaba da mamayar yankunan Lebanon, to dole ne a tunkare ta ta hanyar gwagwarmaya da ayyukan soji.

Shugaban na Hizbullah ya yi nuni da cewa yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma tsakanin Isra’ila da Lebanon a fili take, babu wata boyayyiyar yarjejeniya da aka kulla, komai a bayyane yake.

Ya yi nuni da cewa, yarjejeniyar ta yi magana karara a kan “kudancin kogin Litani” sau biyar, yana mai cewa, “Wannan shi ne tsarin da ya kamata mu bi.”

“Wannan yarjejeniya wani bangare ne na kuduri mai lamba 1701 na Majalisar Dinkin Duniya na dakatar da ta’addancin Isra’ila,” in ji shi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar wakilai na shirin ƙwace rajistar jam’iyyu daga hannun INEC

Majalisar Wakilai na shirin kafa wata sabuwar hukuma da za ta karɓi ikon yin rajistar jam’iyyun siyasa daga Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).

Wannan na zuwa ne bayan da majalisar ta gabatar da wani sabon ƙudiri kan batun.

Sojoji sun hallaka mai haɗa wa Boko Haram bam a Sambisa Dakatarwa: Har yanzu ni Sanata ce — Natasha

Kakakin Majalisar, Hon. Tajudeen Abbas, tare da Hon. Marcus Onobun daga Jihar Edo ne, suka gabatar da ƙudirin.

Ƙudirin na neman kafa wata hukuma mai zaman kanta da za ta riƙa yi wa jam’iyyu rajista, kula da dokokinsu, da kuma tallafa musu.

Har ila yau, ƙudirin na neman a kafa wata kotu ta musamman da za ta duba ƙorafe-ƙorafen da suka shafi jam’iyyu da rikice-rikicen da ke tasowa a tsakaninsu.

A cewar Hon. Marcus Onobun, wannan matakin ya zama dole domin kawo ƙarshen rikice-rikicen cikin gida da ke addabar jam’iyyun siyasa a Najeriya.

A halin yanzu, ƙudirin ya tsallake karatu na biyu a majalisar, lamarin da ke nuni da cewa ana iya ci gaba da duba yiwuwar aiwatar da shi a nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta aike da tawaga zuwa Doha domin ci gaba da tattaunawar sulhun Gaza
  • Isra’ila ta katse wutar lantarki a zirin Gaza
  • Shugabannin Larabawa Sun Amince Da Tsarin Gina Gaza Da Zai Lakume Dala Biliyan 53
  • Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan
  • Al-Houthi: Mun Baiwa Isra’ila Wa’adin Kwanaki 4 Da Ta Kawo Karshen Killace Gaza
  •  Yahudawa 800 Sun Kutsa Cikin Kasar Lebanon A Yau Juma’a
  • Gwamna Inuwa Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Sheikh Sa’eed Jingir
  • Majalisar wakilai na shirin ƙwace rajistar jam’iyyu daga hannun INEC
  • Kotu A Kano Ta Yanke Wa Wata Mata Hukunci Kan Safarar Maƙudan Kuɗaɗe