Pezeshkian: Duk wani rikici a gabas ta tsakiya babbar illa ce ga duniya baki daya
Published: 10th, March 2025 GMT
Shugaba Masoud Pezeshkian ya ce manufar Iran ta ginu ne kan samar da hadin kai a yammacin Asiya, kamar yadda kuma ta yi imanin cewa duk wani rikici da tashin hankali a yankin to zai illata kowa.
Pezeshkian ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da Firaministan Norway Jonas Gahr Støre a yammacin waannan Lahadi, inda suka tattauna kan muhimman batutuwa ad suka shafi alaka tsakanin kasashen biyu, da kuma sauran batutuwa na yankin da kuma na kasa da kasa.
Shugaban na Iran ya kara da cewa, Haramtacciyar Kasar Isra’ila na neman yada karya dangane da batun ayyukan nukiliyar Iran a matsayin tushen rashin tsaro a yankin.
Har ila yau ya jaddada cewa Iran ba ta taba neman kera makaman nukiliya ba.
Shugaba Pezeshkian ya ce Iran ta ba da hadin kai kuma za ta ci gaba da hada kai da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA domin kara tabbatar wa duniya da cewa shirinta na ayyukan farar hula ne, sabanin abin da makiyanta suke yadawa..
A nasa bangaren Firaministan Norway ya ce, kasarsa a shirye take ta ba da duk wani taimako da nufin warware matsalolin da ke faruwa a yankin yammacin Asiya a cikin lumana, tare da kara karfafa alakarta da kasar Iran.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
A ranar Mata Ta Duniya, Hamas Ta Yi Allawadai Da Kashe Mata 12,000 A Gaza
A dai dai lokacinda ake bukukuwan ranar mata ta duniya kungiyar Hamas wacce take iko da Gaza, ta yi allawadi da HKI saboda kissan mata kimani 12.000 a gaza a cikin yakin tufanul Aksa.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kungiyar Hamas na fadar haka a yau Asabar, ta kuma kara da cewa kasashen yamma musamman Amurla da kasashen Turai, idan magana ta zo kan matan Falasdinawa wadanda HKI ta kashe, suna nuna faska biyu. Kashe mata Falasdinawa ba take hakkin mata ne ba, tunda HKI ce ta kashe su.
Kungiyar ta kara da cewa HKI ta kashe mata 12,000 sannan ta raunata wasu dubbai, haka ma ta kori wa su da dama daga godajensu.