Kwallon Mata: Nijeriya Ta Nuna Wa Afrika Ta Kudu Kwanji A Pretoria
Published: 10th, March 2025 GMT
Tawagar matasan yan wasan ƙwallon ƙafa ta Nijeriya ta mata (Flamingos) ta yi nasarar doke mai masaukin baƙi Bantwana ta Afrika ta Kudu da ci 3-1 a wasan farko na gasar cin kofin duniya na mata ‘yan kasa da shekaru 17 na shekarar 2025 a filin wasa na Lucas Moripe, Pretoria a ranar Asabar, in ji jaridar Prompt News.
Shakirat Moshood ce ta jefa wa Nijeriya ƙwallon farko a wasan cikin mintuna 20 kacal da farawa, Harmony Chidi ta ninka damar da Nijeriya ke da ita daga bugun fanareti mintuna biyar kafin a tafi hutun rabin lokaci.
Cinikayyar ‘Yan Kwallon Da Aka Yi A Watan Janairu Hadin Gwiwar Sin Da Nijeriya Za Ta Ba Mata Damar Cimma BurikansuAfrika ta Kudu ta dawo daga hutun rabin lokaci cikin azama da sa rai ta kuma rage giɓin dake tsakanin ƙasashen biyu bayan an dawo daga hutun rabin lokaci, kyaftin ɗin tawagar Afrika ta Kudu Success Malebana ne ta ci daga bugun fenariti.
Chidi kuma ta ƙara jefawa Nijeriya ƙwallo a ragar masu masauƙin baƙin a minti na 68, kungiyoyin biyu za su sake karawa ne a fafatawar da za a yi a filin wasa na Remo Stars, Ikenne mako mai zuwa ranar Asabar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Likitocin Nijeriya dubu 16 sun yi ƙaura zuwa ƙetare — Ministan Lafiya
Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Pate ya bayyana cewa, sama da likitoci dubu 16 sun fice daga Nijeriya a cikin shekaru biyar zuwa bakwai da suka gabata zuwa wasu ƙasashen duniya don ci gaba da aiki cikin ingantaccen yanayi.
Farfesa Pate ya bayyana haka ne a wurin taron horas da Ƙungiyar Likitocin Afrika da ya gudana a birnin Abuja a ranar Talata.
Nijar ta ayyana Hausa a matsayin yaren ƙasa DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’Ministan ya bayyana cewa, ana ci gaba da samun wani adadi mai yawa na ƙwararrun likitocin da ke da burin fita zuwa wasu ƙasashen duniya aiki, suna fakewa da matsalolin tattalin arziƙi da rashin kyawun yanayin aiki da kuma samun cikakken horo, baya ga zurfafa gudanar da bincike a ƙasashen na ƙetare.
Kodayake ya ce, ficewar ƙwararrun likitoci daga ƙananan ƙasashe zuwa ƙasashen da suka ci gaba, ba sabon labari ba ne, amma sai dai adadinsu na ƙara yawaita a shekarun baya-baya nan a cewarsa.
Pate ya kuma bayyana takaicinsa kan yadda su ma nas-nas da unguwarzoma suka fice daga ƙasar, lamarin da ya ƙara zabtare adadin ma’aikatan lafiyar da ake da su a Najeriya.
A cewar Ministan Lafiyar, kididdiga ta nuna kusan likitoci huɗu ne ke duba mutum dubu 10 a ƙasar, yana mai ƙiyasta sama da Dala dubu 21 a matsayin kuɗin da ake kashe wa kowanne likita guda wajen horas da shi.
“A Najeriya kaɗai, sama da likitoci dubu 16 aka ƙiyasta sun fice daga ƙasar a cikin shekaru biyar zuwa bakwai. Nas-nas da unguwarzoma su ma sun yi ƙaranci.
“Yanzu likita kusan huɗu ne ke duba mutum dubu 10, adadin da ya yi ƙasa sosai idan aka kwatanta da alkaluman da aka amince da su a matakin duniya.”