HausaTv:
2025-03-10@12:09:01 GMT

Isra’ila ta katse wutar lantarki a zirin Gaza

Published: 10th, March 2025 GMT

Gwamnatin Isra’ila ta sanar da katse wutar lantarki a Zirin Gaza.

Ministan Makamashi na Isra’ila Eli Cohen ne ya sanar da matakin da gwamnatin kasar ta dauka na katse wutar lantarki a zirin, a yayin da wasu rahotanni ke cewa mataki na gaba bayan katsewar wutar lantarkin, shi ne yanke ruwa a arewacin zirin Gaza.

Ya ce matakin da gwamnatin kasar ta dauka na kara kaimi ne domin kwato dukkan mutanen da ake garkuwa dasu tare da tabbatar da cewa Hamas ba za ta ci gaba da zama a Gaza ba bayan yakin.

A daya banagaren kuma Ministan kudi na Isra’ila ya yi ikirarin cewa gwamnatin kasar za ta hada kai da gwamnatin Amurka karkashin jagorancin Donald Trump domin sanin kasashen da za su karbi bakoncin bakin haure daga Gaza.

A baya-bayan nan ne shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar da shirin tilastawa mazauna yankin Zirin Gaza zuwa kasashen Jordan da Masar da ke makwabtaka da ita.

Shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi da Sarkin Jordan Abdallah na biyu sun yi kakkausar suka ga shirin mamayar tare da jaddada cewa ba za su iya karbar sabbin ‘yan gudun hijira ba.

Jami’an kasashen Jordan da Masar da kuma wasu kasashen Larabawa sun jaddada cewa dole ne a kafa kasar Falasdinu, kuma a bar al’ummarta su zabi makomarsu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Qatar Ta Ce Bata Goyon Bayan Yakin Don Warware Shirin Nukliyar Kasar Iran

Ministan harkokin wajen kasar Qatar Mohammad Bin Abdurrahman Al-Thani, ya kara nanata matsayin kasar na kin duk wani yaki kan shirin Nukliyar kasar Iran, ya kuma yi kira ga Amurka da Iran su warware wannan matsalar ta ruwan sanyi. Ko hanyar diblomasiyya.

Kafin haka dai JMI ta sha nanata cewa shirinta na makamashin na zaman lafiya ne. Sannan don haka ne ta amince ta kulla yarjeniyar shirin nukliya ta zaman lafiya  da manya manyan kasashen duniya, a shekara ta 2015 daga ciki har da kasar Amurka. Amma shugaban kasar Amurka na lokacin Donql Trump ta fidda kasar daga yarjeniyar sannan ta dorawa kasar takunkuman tattalin arziki mafi muni don tursasa mata ta sake zama don sabuwar tattaunawa da ita.

Mohammed bin Abdulrahman Al Thani yace “akwai bukatar kasashen Iran da Amurka su fahinci juna a cikin wannan batun” sannan ya sake nanata cewa Qatar bata goyon bayan yaki. Sannan daga karshe yace matsalar nukliyar kasar Iran ta zama abinda damuwa ga dukkan kasashen yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta aike da tawaga zuwa Doha domin ci gaba da tattaunawar sulhun Gaza
  • Qatar ta yi kira ga hukumar IAEA da ta sanya ido kan cibiyoyin nukiliyar Isra’ila
  • New York Times: Isra’ila ce ta kashe wasu fursunoninta da ake tsare da su a Gaza
  • Sharhin Bayan Labarai: Kasashen Afirka Sun Kori Sojojin Faransa Daga Kasashensu
  • Kasashen Turai sun goyi bayan shirin Larabawa na sake gina Gaza
  • Amurka : Trump Ya Katse Tallafin Jami’ar Columbia, Saboda Zanga-zangar Goyon Bayan Falasdinu
  • Qatar Ta Ce Bata Goyon Bayan Yakin Don Warware Shirin Nukliyar Kasar Iran
  • Sojojin Isra’ila Sun Kai Hari A Kan Masallatan Nablus A Ranar Juma’ar Farko Ta Watan Ramadan
  • OIC Ta Yi Maraba Da Shirin Gwamnatocin Larabawa Na Sake Gina Zirin Gaza