Kasar Qatar ta bukaci hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa da ta sanya ido kan cibiyoyin nukiliyar Isra’ila.

A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta fitar ta bayyana cewa, Doha ta bukaci hukumar ta (IAEA) da ta sanya damar gudanar da bincike da ka’ida daga hukumar ta MDD, kan dukkanin cibiyoyin nukiliyar Isra’ila.

Jakadan dindindin na Qatar a Majalisar Dinkin Duniya, Jasem Yacoub al-Hammadi, ya bukaci gwamnatin Isra’ila da ta rattaba hannu kan yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya (NPT).

Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta fitar ta ce “Al-Hammadi ya jaddada bukatar kasashen duniya da cibiyoyinta su tabbatar da alkawurran da suka dauka a karkashin kudurorin kwamitin sulhu na MDD, da babban taron MDD, da hukumar IAEA da kuma taron bitar NPT na shekarar 1995, wanda daga bisani ya bukaci Isra’ila da ta mika dukkanin cibiyoyinta na nukiliya ga tsarin kiyaye zaman lafiya na IAEA.”

Ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta ce jakadan Qatar ya yi kira da a kara kaimi ga kokarin da kasashen duniya ke yi na shigar da Isra’ila cikin tsarin NPT.

Sanarwar ta kara da cewa, dukkan kasashen Gabas ta Tsakiya, in ban da gwamnatin Isra’ila, suna cikin yarjejeniyar NPT, ta hana yadfuwar makamman nukiliya.

An dai bayyana cewa Isra’ila tana da manyan makaman nukiliya tsakanin 200 zuwa 400 a ma’ajiyar makamanta, wanda hakan ya sa ta kasance kasa daya tilo mai mallakar makaman nukiliya a yammacin Asiya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hisbah ta warware rigingimu 565 da lalata katan 51 na barasa a Yobe

Hukumar Hisbah ta Jihar Yobe ta ce, ta warware rigingimu 565 a cikin watanni 12 da suka gabata a jihar.

Wannan hukuma dai gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ne ya kafa ta a watan Maris, 2024 a wani ɓangare na ƙoƙarin magance munanan ɗabi’u a jihar.

Trust Radio 92.7FM za ta fara shirye-shiryen gwaji An kama masu garkuwa da mutane biyu a Yobe

Shugaban Hukumar ta Hisbah, Dakta Yahuza Hamza Abubakar, ya ce matsalolin da aka warware sun haɗa da batutuwan da suka shafi: Harkar iyali da kasuwanci da gado da kuma basussuka.

Sauran matsalolin da hukumar ta Hisbah ke warwarewa sun haɗa da: Matsalolin da haddasa rikicin manoma da makiyaya da kuma rashin biyan kuɗin haya.

A cewarsa, an warware akasarin shari’ar ta hanyar sulhu da fahimtar juna.

Dokta Hamza ya ce, jami’an hukumar sun kuma ƙwace kwalayen barasa guda 56 da kuma 18 na sinadaran fosters na methylene chloride chemical (Madarar Sukurdai) a faɗin jihar.

Ya ce, addinin Musulunci da dokar da ta kafa hukumar a shekarar 2024 ta haramta sayar da barasa da sauran kayan maye a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hisbah ta warware rigingimu 565 da lalata katan 51 na barasa a Yobe
  • Jami’an Amurka da na Saudiyya sun tattauna batutuwan da suka shafi Gaza da yankin
  • Pezeshkian : Jagora bai shi da adawa da Amurkawa masu zuba jari a Iran
  • Amurka ta laftawa Iran sabbin takunkumai gabanin tattaunawar Oman
  • Al’ummar Karamar Hukumar Maigatari Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Gina Musu Hanyoyi
  • Gaza: Isra’ila ta kashe fararen hula 58 a cikin ‘yan sa’o’i da suka gabata
  • An kori jakadan Isra’ila a Habasha daga taron Tarayyar Afirka
  • Gaza: Isra’ila ta kashe Falasdinawa 58 a awa 58
  • Gaza: Isra’ila ta kashe Falasindawa 58 a awa 58
  • Dan jarida Ahmad Mansour ya yi shahada bayan sojojin Isra’ila sun kona shi da ransa a Gaza